ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jama’ar Yobe Sun Nuna Rashin Gamsuwarsu Kan Ayyukan Kananan Hukumomin Jihar —Bincike

by Muhammad Maitela
4 years ago
Yobe

A wani sabon rahoto ya nuna yadda al’ummar jihar Yobe, dake Arewa Maso Gabashin Nijeriya suka nuna rashin gamsuwarsu da rashin sauke nauyin da ya hau wuyan kananan hukumomin jihar, tare da bukatar samun ingantuwar muhimman ayyukan raya yankunan karkara wanda ya rataya bisa wuyan kananan hukumomin.

Rahoton wanda aka yiwa taken: Rahoton Ayyukan Kananan Hukumomin Jihar Yobe, ya saurari ra’ayoyin al’ummar jihar dangane da tabbatar da gamsuwa ko rashin gamsuwa da ayyukan kananan hukumomin.

  • Sanata Gaidam Ya Talllafa Wa Matasa 400 A Mazabarsa Da Kayan Sana’o’in Dogaro Da Kai A Yobe

Sakamakon binciken, da aka fitar a ranar 18 ga watan Oktoba 2022, wanda kungiyar YMonitor ce ta gudanar dashi – wadda ke bibiya tare da tabbatar da ingantuwar tsarin Shugabanci da hadin gwiwa da kungiyar ‘The Future Project’ (TFP), wanda ya samu tallafin kungiyar ‘National Endowment for Democracy’.

ADVERTISEMENT

A cikin takardar sanarwar da Shugaban dake jagorantar aikin YMonitor, Omidiji Olamilekan ya fitar yace, baya ga auna gamsuwar al’umma kan ayyukan kananan hukumominsu, rahoton har ila yau ya wayar da kan al’umma wajen sanin aikace-aikacen da suka rataya ga kananan hukumomin.

Bugu da kari kuma, binciken ya kunshi shawarwari ga hukumomi wajen farfado da tsarin kananan hukumomi a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Haka kuma, jwabin nasa ya zayyano sakamakon binciken wanda ya bayyana yadda al’umma suka nuna rashin gamsuwarsu da Shugabannin Kananan Hukumomi, inda sakamakon binciken ya gano yadda jama’ar ke nuna tsananin damuwa a kan harkokin siyasa da kuma sanin ayyukan kananan hukumomin a tsakanin al’ummar jihar Yobe.

Jagoran wannan binciken, Omidiji Olamilekan ya ce, “Wannan rahoton zai taimaki shugabannin kananan hukumomi wajen gano matsayin da suke, amfani da damar da suke da ita wajen daukar matakan da ya dace don cike gibin da ake dashi cikin hanzari tare da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.”

Har wala yau kuma, ta hanyar amfani da na’aurar bincike ta ‘Net Promoter Score Test’, sakamakon binciken ya bayyana yadda jama’ar jihar Yobe suka ki amincewa da nada Shugabannin kananan hukumomin jihar zuwa wasu manyan mukamai na gaba.

Inda a karshe binciken ya bayar da shawarar cewa akwai bukatar gwamnati ta shirya tarukan karawa juna sani ga Shugabannin Kananan Hukumomi domin samun kwarewar zamani da duniya ke amfani dashi yanzu.

Yobe
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Kwankwaso Zai Bayyana Manufofin Takararsa A Ranar 1 Ga Watan Nuwamba

Kwankwaso Zai Bayyana Manufofin Takararsa A Ranar 1 Ga Watan Nuwamba

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.