ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jama’ar Yobe Sun Nuna Rashin Gamsuwarsu Kan Ayyukan Kananan Hukumomin Jihar —Bincike

by Muhammad Maitela
4 years ago
Yobe

A wani sabon rahoto ya nuna yadda al’ummar jihar Yobe, dake Arewa Maso Gabashin Nijeriya suka nuna rashin gamsuwarsu da rashin sauke nauyin da ya hau wuyan kananan hukumomin jihar, tare da bukatar samun ingantuwar muhimman ayyukan raya yankunan karkara wanda ya rataya bisa wuyan kananan hukumomin.

Rahoton wanda aka yiwa taken: Rahoton Ayyukan Kananan Hukumomin Jihar Yobe, ya saurari ra’ayoyin al’ummar jihar dangane da tabbatar da gamsuwa ko rashin gamsuwa da ayyukan kananan hukumomin.

  • Sanata Gaidam Ya Talllafa Wa Matasa 400 A Mazabarsa Da Kayan Sana’o’in Dogaro Da Kai A Yobe

Sakamakon binciken, da aka fitar a ranar 18 ga watan Oktoba 2022, wanda kungiyar YMonitor ce ta gudanar dashi – wadda ke bibiya tare da tabbatar da ingantuwar tsarin Shugabanci da hadin gwiwa da kungiyar ‘The Future Project’ (TFP), wanda ya samu tallafin kungiyar ‘National Endowment for Democracy’.

ADVERTISEMENT

A cikin takardar sanarwar da Shugaban dake jagorantar aikin YMonitor, Omidiji Olamilekan ya fitar yace, baya ga auna gamsuwar al’umma kan ayyukan kananan hukumominsu, rahoton har ila yau ya wayar da kan al’umma wajen sanin aikace-aikacen da suka rataya ga kananan hukumomin.

Bugu da kari kuma, binciken ya kunshi shawarwari ga hukumomi wajen farfado da tsarin kananan hukumomi a Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Haka kuma, jwabin nasa ya zayyano sakamakon binciken wanda ya bayyana yadda al’umma suka nuna rashin gamsuwarsu da Shugabannin Kananan Hukumomi, inda sakamakon binciken ya gano yadda jama’ar ke nuna tsananin damuwa a kan harkokin siyasa da kuma sanin ayyukan kananan hukumomin a tsakanin al’ummar jihar Yobe.

Jagoran wannan binciken, Omidiji Olamilekan ya ce, “Wannan rahoton zai taimaki shugabannin kananan hukumomi wajen gano matsayin da suke, amfani da damar da suke da ita wajen daukar matakan da ya dace don cike gibin da ake dashi cikin hanzari tare da sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.”

Har wala yau kuma, ta hanyar amfani da na’aurar bincike ta ‘Net Promoter Score Test’, sakamakon binciken ya bayyana yadda jama’ar jihar Yobe suka ki amincewa da nada Shugabannin kananan hukumomin jihar zuwa wasu manyan mukamai na gaba.

Inda a karshe binciken ya bayar da shawarar cewa akwai bukatar gwamnati ta shirya tarukan karawa juna sani ga Shugabannin Kananan Hukumomi domin samun kwarewar zamani da duniya ke amfani dashi yanzu.

Yobe
Muhammad Maitela
+ postsBio
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    29 Ga Mayu: Gwamna Buni Zai Yi Tattaunawar Kai Tsaye Ta Farko Da Al’umma
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    Wakilin VOA Haruna Dauda Ya Rasu A Maiduguri
  • Muhammad Maitela
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-maitela/
    PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Kwankwaso Zai Bayyana Manufofin Takararsa A Ranar 1 Ga Watan Nuwamba

Kwankwaso Zai Bayyana Manufofin Takararsa A Ranar 1 Ga Watan Nuwamba

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.