• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 69 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 69 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Akalla mutane 69 ne aka samu nasarar ceto su daga hannun masu garkuwa da mutane a jihar Bauchi sakamakon aikin hadin guiwa tsakanin jami’an tsaro da kungiyoyin sa-kai irin su ‘yan Bijilante da ‘yan Nanga wadanda suka kutsa kai maboyar masu garkuwan a cikin dazuka tare da ceto mutanen.

Wannan bayanin ya fito daga bakin kwamishinan kananan hukumomi da kula da Masarautun gargajiya na jihar Bauchi, Hon. Abdulrazaq Nuhu Zaki yayin da ke ganawa da ‘yan jarida a jiya.

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 32 Daga Masu Garkuwa
  • Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan

Ya ce, tun lokacin da aka fara samun ‘yan matsalolin tsaro a jihar gwamnati da sarakuna hadi da jami’an tsaro tare da shugabannin kananan hukumomi suka bazama kokarin dakile aniyar bata-garin inda suka cimma muhimman nasarori kan hakan.

Ya ce, jami’an tsaron sun yi ta sintiri zuwa dazukan da ‘yan ta’addan ke fakewa inda suka fatattaki wasu tare da ceto wadanda suka yi garkuwa da su da dama.

A kan hakan ya ce yanzu jihar Bauchi ta samu kwanciyar hankali daga barazanar masu garkuwa da mutane, “Domin koda wasa gwamna Bala Muhammad baya sakaci da harkokin da suka shafi tsaro. Lamari na tsaro na faruwa zai tashi tsaye.”

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

A cewarsa an samu kwararowar ‘yan garkuwa da mutane cikin dazuka a Toro, Alkaleri, Tafawa Balewa da karamar hukumar Ningi wanda kuma tunin hukumomi suka yi abubuwan da suka dace domin dakile yunkurin su. Yana mai cewa wasu ma ba ‘yan jihar Bauchi ba ne.

A cewarsa: “Gwamna Bala Muhammad da kansa yake jagorantar yaki da wannan matsalar. Ya sha ziyartar yankunan da matsalar ya shafa tare da jajanta musu da kuma karfafa musu guiwar su dake su jajirce wajen tunkarar masu garkuwan daidai da karfinsu. Hakan ya kara wa jama’a kumaji da farkawa.

“Da hadin guiwar shugabannin kananan hukumomin jihar da shi kansa gwamnan Bala Muhammad da jami’an tsaro muna kan magance ‘yan kananan matsalolin tsaro da suke akwai. Domin shi gwamna bai wasa ko kadan a kan hidimar tsaro. Domin shi gwamnan ya karfafi masu ruwa da tsaki kan yin abun da ya dace.

“A wannan fatattakar da aka yi wa ‘yan ta’addan an samu nasarar kwato mutane 69 a sassa daban-daban na jihar Bauchi.”

Nuhu Zaki ya ce tunin gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad ya fara tattaunawa da Gwamnatin jihar Fitato da Taraba da suka iya iyaka da jihar domin ganin an hada kai wajen yin sintirin hadin guiwa domin kawo karshen ‘yan ta’addan da ke buya a cikin dazukan jihohin ukun.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiGarkuwaGwamnatin BauchiJami'an TsaroYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 32 Daga Masu Garkuwa

Next Post

Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

Related

Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

20 minutes ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

1 hour ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

3 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

4 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

6 hours ago
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

9 hours ago
Next Post
Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.