• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 69 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Jami'an Tsaro

Akalla mutane 69 ne aka samu nasarar ceto su daga hannun masu garkuwa da mutane a jihar Bauchi sakamakon aikin hadin guiwa tsakanin jami’an tsaro da kungiyoyin sa-kai irin su ‘yan Bijilante da ‘yan Nanga wadanda suka kutsa kai maboyar masu garkuwan a cikin dazuka tare da ceto mutanen.

Wannan bayanin ya fito daga bakin kwamishinan kananan hukumomi da kula da Masarautun gargajiya na jihar Bauchi, Hon. Abdulrazaq Nuhu Zaki yayin da ke ganawa da ‘yan jarida a jiya.

  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 32 Daga Masu Garkuwa
  • Babu Nasara Ga ’Yan Awaren Taiwan

Ya ce, tun lokacin da aka fara samun ‘yan matsalolin tsaro a jihar gwamnati da sarakuna hadi da jami’an tsaro tare da shugabannin kananan hukumomi suka bazama kokarin dakile aniyar bata-garin inda suka cimma muhimman nasarori kan hakan.

Ya ce, jami’an tsaron sun yi ta sintiri zuwa dazukan da ‘yan ta’addan ke fakewa inda suka fatattaki wasu tare da ceto wadanda suka yi garkuwa da su da dama.

A kan hakan ya ce yanzu jihar Bauchi ta samu kwanciyar hankali daga barazanar masu garkuwa da mutane, “Domin koda wasa gwamna Bala Muhammad baya sakaci da harkokin da suka shafi tsaro. Lamari na tsaro na faruwa zai tashi tsaye.”

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

A cewarsa an samu kwararowar ‘yan garkuwa da mutane cikin dazuka a Toro, Alkaleri, Tafawa Balewa da karamar hukumar Ningi wanda kuma tunin hukumomi suka yi abubuwan da suka dace domin dakile yunkurin su. Yana mai cewa wasu ma ba ‘yan jihar Bauchi ba ne.

A cewarsa: “Gwamna Bala Muhammad da kansa yake jagorantar yaki da wannan matsalar. Ya sha ziyartar yankunan da matsalar ya shafa tare da jajanta musu da kuma karfafa musu guiwar su dake su jajirce wajen tunkarar masu garkuwan daidai da karfinsu. Hakan ya kara wa jama’a kumaji da farkawa.

“Da hadin guiwar shugabannin kananan hukumomin jihar da shi kansa gwamnan Bala Muhammad da jami’an tsaro muna kan magance ‘yan kananan matsalolin tsaro da suke akwai. Domin shi gwamna bai wasa ko kadan a kan hidimar tsaro. Domin shi gwamnan ya karfafi masu ruwa da tsaki kan yin abun da ya dace.

“A wannan fatattakar da aka yi wa ‘yan ta’addan an samu nasarar kwato mutane 69 a sassa daban-daban na jihar Bauchi.”

Nuhu Zaki ya ce tunin gwamnan Jihar Bauchi Bala Muhammad ya fara tattaunawa da Gwamnatin jihar Fitato da Taraba da suka iya iyaka da jihar domin ganin an hada kai wajen yin sintirin hadin guiwa domin kawo karshen ‘yan ta’addan da ke buya a cikin dazukan jihohin ukun.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140
Labarai

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Majalisar Dattawa
Labarai

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Next Post
Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

Yadda Matuka Jirgi Suka Shantake Da Bacci A Lokacin Sauka

LABARAI MASU NASABA

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025
Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.