Jami’ar Jos ce ta zama gwarzon gasar wasannin ma’aikatan jami’o’in Nijeriya karo na 14 (NUSSA), wadda Jami’ar Bayero da ke Kano ta karɓi bakuncinta. Jami’ar ta Jos ta lashe lambobin yabo guda 13, ciki har da Zinare 7, Azurfa 3 da Tagulla 3, wanda ya ba ta damar darewa saman teburin nasarori.
A matsayi na biyu kuma, Jami’ar Ahmadu Bello, Zaria, ta samu nasarar lashe lambobin yabo 12 – zinare 6, azurfa 3 da tagulla 3. Jami’ar Tarayya ta Dutsinma ta zo ta uku da zinare 4, azurfa 4 da tagulla 5.
- Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo
- Kyawawan Halayen Annabawa Da Ke Nuni Da Cikarsu (AS)
Babban abin da ya dauki hankali a gasar karshe da aka gudanar a ranar Juma’a, 30 ga Mayu, 2025, shi ne wasan karshe na kwallon kafa tsakanin Jami’ar Tarayya ta Harkokin Sufuri, Daura da Jami’ar Tarayya, Dutsinma. Bayan wasan ya kare 1-1, FUT Daura ta doke Dutsinma da ci 3-1 a bugun fenareti, inda ta lashe zinaren kwallon kafa.
Wannan gagarumar nasara da Jami’ar Jos ta samu na kara tabbatar da jajircewar jami’ar wajen bunkasa wasanni a tsakanin ma’aikata, da kuma karfafa dankon zumunci da kwarewa a tsakanin jami’o’in kasar nan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp