ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

by Abubakar Abba
1 year ago
Zulum

Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya yi kira ga Hukumar Raya Yankin Tafkin Chadi, ta zuba hannun jari a bangaren noman rani a tafkin yankin na Chadi.

Zulum ya sanar da haka ne, a lokacin da yake karbar bakuncin sabbin mahukunta na Hukumar Bunkasa Yankin Tafkin Chadi, a fadar gwamnatin jihar ta Borno da ke Maiduguri, babban birnin jihar.

  • Darajar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso Shida Bisa Dari A Afirilu
  • Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Har ila yau, gwamnan ya bukaci zuba hannun jarin, musaman a yankunan Kirenowa, Marte, Gamborun Ngala da kuma Baga.

ADVERTISEMENT

Zulum ya yi nuni da cewa, zuba hannun jarin zai taimaka matuka da gaske, wajen bunkasa wadataccen abinci da kuma farfado da tattalin arziki a jihar da ma yankin Arewa Maso Gabashin wannan kasa baki- daya.

“Ba zai taba yiwuwa mu ci gaba da dogara kacokan a kan ruwan da muke samu ba, inda ya kara da cewa; bincikenmu ya tabbatar mana da cewa, ruwan da ake samu daga tafkin Chadi na da matukar yawan gaske, wanda idan muka mayar da hankali yadda ya kamata, ko shakka babu, za mu iya jawo ruwan ta hanyar yin amfani da injinoni,” in ji Zulum.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Haka zalika, ya kara da cewa; gwamnatinsa ta bayar da kimanin Naira biliyan biyu, domin noma hekta 1,000 na gonaki ta hanyar amfani da na’urar noman rani mai amfani da hasken rana a garin Baga.

Gwamna Zulum ya ci gaba da cewa, kwanan nan ya tura wata tawagar bincike, don yin bincike tare da gano gaskiya zuwa Gamborun Ngala, sannan kuma tawagar ta tabbatar mana da samun albarkatun ruwan karkashin kasa, wadanda za mu iya amfani da su wajen noman rani ta hanyar ban-ruwa.

Kazalika, ya sanar da cewa, an kuma kebe karin wasu Naira biliyan 1.5, domin gudanar da irin wadannan ayyuka a garuruwan Gamborun Ngala da Marte, wadanda a halin yanzu an kusa kammala su baki-daya.

Bugu da kari, ya bayyana cewa; bisa kokarin gwamnatinsa na mayar da hankali wajen farfado da shirin noman rani na Tafkin Chadi ta Kudu, tuni aka fara noma hekta 1,000 a karkashin aikin noma na Baga a kan kudi kimanin Naira biliyan biyu.

Gwaman ya ci gaba da cewa, har ila yau; gwamnatin jihar ta Borno ta samar da hekta 200,000 a Gamboru da kuma wata hekta 200,000 na samar da wutar lantarki a Lamboru ta hanyar amfani da tsarin ban-ruwa, domin farfado da ayyukan noma a fadin yankin baki-daya.

Haka zalika, Zulum ya sanar da cewa, gwamnatinsa ta haka rijiyoyi kusan kimanin 3,000 a Damasak da ke Karamar Hukumar Mobba.

Sannan kuma, ya yi nuni da cewa; wannan ya bai wa manoma da dama damar yin noma a fili mai tsawon kilomita 16, matakin da ya bullo da hanyar noman ruwan karkashin kasa a yankin da a baya ba a saba yin irin sa ba.

Zulum ya kuma yi alkawarin ci gaba da hada kai da hukumar, musamman domin samun nasarar fadada noman a Ngala da Damasak da sabon yankin Marte tare da samar da ababen more rayuwa ga al’ummar yankin da suka dawo yankin da kuma tabbatar da dorewar samar da wadataccen abinci.

Gwamnan ya kuma sanar da cewa, gwamnatinsa na ci gaba da tallafawa wajen farfado da tashar famfunan ruwa da ke Chadi Basin Kirenowa.

A cewarsa, gwamnatinsa na kan kokarin ganin ganin an kafa bataliyar soji a yankin, musamman don inganta tsaro tare da samun zaman lafiya, inda ya kara da cewa; gwamnatin tasa za ta so sanin inda za a iya shiga, sakamakon cewa abubuwan da za a iya samu suna nan.

Ya kara da bayyana cewa, yana ci gaba da tuntubar shugaban kasa da sauran shugabannin sojoji, kan yiwuwar kafa bataliyar soji a Kirenowa da nufin kare tashar famfon.

A nasu jawaban daban-daban tunda farko, shugaban hukumar, Farfesa Abdu Dauda Biu da Manajan Darakta, Alhaji Tijjani Tumsa sun sanar da gwamnan cewa; an kafa sabuwar hukumar ce a ranar 13 ga watan Disamba 2024.

A cewarsu, wannan ziyara na da matukar muhimmancin gaske, duba da cewa; wuraren da ke karkashin kulawarsu, ciki har da madatsar ruwa ta Alau, na samun kulawar da ta dace.

Kazalika, sun kuma jinjina wa Zulum; kan yadda yake gudanar da ayyukansa da kuma jajircewarsa, musamman a wannan bangare na madatsun ruwa da ke wannan jiha.

Har ila yau, shugabancin hukumar ya yi alkawarin hada kai da gwamnatin jihar ta Borno, musamman don samun nasarar aiwatar da wadannan ayyuka da suka shafi noman rani da kiwon dabbobi da kuma kamun kifi a wadannan yankuna.

Haka zalika, sun kuma bukaci goyon bayan Gwamna Zulum, wajen ganin an kammala wannan gyara na madatsar ruwa ta Alau a kan lokaci, wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da shi a ‘yan kwanakin baya.

Zulum
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.