• English
  • Business News
Wednesday, July 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar APC A Kano Na So A Hukunta Bashir Ahmad Kan Halartar Gasar Cin Kofin Duniya A Qatar

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Jam’iyyar APC A Kano Na So A Hukunta Bashir Ahmad Kan Halartar Gasar Cin Kofin Duniya A Qatar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC, a Jihar Kano sun bukaci shugabannin jam’iyyar da su gaggauta daukar tsauraran matakai kan mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad, bisa zarginsa da rashin mutunta jam’iyyar na kin halartar taron kaddamar da yakin neman zabenta a jihar.

Mambobin sun zargi Bashir Ahmad da zabar  wasan gasar cin kofin duniya da ake yi a kasar Qatar a daidai lokaci da jam’iyyar ke kokarin kaddamar da yakin zabenta a jihar.

  • Asirin Namiji Mai Zamba Da Shigar Mata Ya Tonu
  • ‘Yan Siyasa Da Masu Zabe: Wane Gauta Ne Ba Ja Ba?

Alhaji Samani Inuwa, daya daga cikin shugabannin jam’iyyar daga karamar hukumar Gaya, ya shaida wa manema labarai tare da wasu mambobin jam’iyyar cewa lamarin Ahmad ya wuce gona da iri.

Ya ce, “Ba mu fahimci yadda Bashir Ahmad ya zabi zuwa Qatar a lokacin da muke Kano muna karamar hukumar Gaya domin kaddamar da yakin neman zaben gwamna da sauran mukamai na jam’iyyar.

“Idan kowane dan jam’iyyar zai yi yadda Bashir ya yi, ba ma tunanin APC za ta kai ga lashe zabe, don haka ya kamata a gaggauta hukunta shi don ya zama darasi ga wasu.”

Labarai Masu Nasaba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Haka zalika shugabannin jam’iyyar sun taya gwamna Abdullahi Ganduje murnar ganin an gudanar da yakin neman zaben gwamna a garin Gaya cikin kwanciyar hankali, inda suka tabbatar da cewa duk da rashin jituwar irin su Bashir Ahmad, APC ce za ta lashe zabe a Kano.

Bashir Ahmad, mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin yada labarai ta yanar gizo, ya wallafa hotonsa a shafinsa na Twitter a wani filin wasa da ke Qatar yana kallonq wasan gasar cin kofin duniya.

Hoton ya janyo cece-kuce yayin da ‘yan jam’iyyar suka bayyana matakin da ya dauka a matsayin abin takaici.

Kokarin jin ta bakin Ahmad ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBashir AhmadkanoQatarYakin Neman Zabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Asirin Namiji Mai Zamba Da Shigar Mata Ya Tonu

Next Post

An Shirya Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Matasan Sin Da Afirka Karo Na Biyu Ta Kafar Bidiyo

Related

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba
Manyan Labarai

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

2 hours ago
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820
Manyan Labarai

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

4 hours ago
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki
Manyan Labarai

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

5 hours ago
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo
Manyan Labarai

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

15 hours ago
Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC
Manyan Labarai

Sauyin Sheƙa Ya Mamaye PDP Da Sauran Jam’iyyu A Borno, Ana Ta Shiga ADC

16 hours ago
ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
Manyan Labarai

ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni

22 hours ago
Next Post
An Shirya Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Matasan Sin Da Afirka Karo Na Biyu Ta Kafar Bidiyo

An Shirya Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Matasan Sin Da Afirka Karo Na Biyu Ta Kafar Bidiyo

LABARAI MASU NASABA

Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza

July 9, 2025
Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

Sanata Natasha Ta Bayyana Dalilin Da Ya Sa Ba Ta Koma Majalisa Ba

July 9, 2025
Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

Dangote Ya Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa Naira 820

July 9, 2025
Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

Kofin Duniya: Chelsea Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Ta Doke Fluminense

July 9, 2025
Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

Malaman Firamare Sun Janye Yajin Aiki A Abuja, An Umarci Su Koma Bakin Aiki

July 9, 2025
Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

Sin Ta Ware Yuan Biliyan 10 Don Shirye-Shiryen Ba Da Tallafin Aiki

July 9, 2025
Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

Tinubu Ba Zai Yarda Hayaniyar Siyasar 2027 Ta Ɗauke Masa Hankali Ba – Ministan Yaɗa Labarai

July 8, 2025
Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa

July 8, 2025
Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

Babatun Lai Ching-Te Ba Zai Taba Girgiza Kasancewar Sin Day Tak A Duniya Ba

July 8, 2025
Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

Igbo Ne Ke Aikata Laifuka A Kudu, Ba Fulani Makiyaya Ba – Gwamna Soludo

July 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.