• Leadership Hausa
Tuesday, February 7, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Manyan Labarai

Jam’iyyar APC A Kano Na So A Hukunta Bashir Ahmad Kan Halartar Gasar Cin Kofin Duniya A Qatar

by Sadiq
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Jam’iyyar APC A Kano Na So A Hukunta Bashir Ahmad Kan Halartar Gasar Cin Kofin Duniya A Qatar

Wasu ‘ya’yan jam’iyyar APC, a Jihar Kano sun bukaci shugabannin jam’iyyar da su gaggauta daukar tsauraran matakai kan mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad, bisa zarginsa da rashin mutunta jam’iyyar na kin halartar taron kaddamar da yakin neman zabenta a jihar.

Mambobin sun zargi Bashir Ahmad da zabar  wasan gasar cin kofin duniya da ake yi a kasar Qatar a daidai lokaci da jam’iyyar ke kokarin kaddamar da yakin zabenta a jihar.

  • Asirin Namiji Mai Zamba Da Shigar Mata Ya Tonu
  • ‘Yan Siyasa Da Masu Zabe: Wane Gauta Ne Ba Ja Ba?

Alhaji Samani Inuwa, daya daga cikin shugabannin jam’iyyar daga karamar hukumar Gaya, ya shaida wa manema labarai tare da wasu mambobin jam’iyyar cewa lamarin Ahmad ya wuce gona da iri.

Ya ce, “Ba mu fahimci yadda Bashir Ahmad ya zabi zuwa Qatar a lokacin da muke Kano muna karamar hukumar Gaya domin kaddamar da yakin neman zaben gwamna da sauran mukamai na jam’iyyar.

“Idan kowane dan jam’iyyar zai yi yadda Bashir ya yi, ba ma tunanin APC za ta kai ga lashe zabe, don haka ya kamata a gaggauta hukunta shi don ya zama darasi ga wasu.”

Labarai Masu Nasaba

Karancin Mai: Kungiyoyin Sufuri Za Su Yi Zanga-Zanga A Hedikwatar NNPC 

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

Haka zalika shugabannin jam’iyyar sun taya gwamna Abdullahi Ganduje murnar ganin an gudanar da yakin neman zaben gwamna a garin Gaya cikin kwanciyar hankali, inda suka tabbatar da cewa duk da rashin jituwar irin su Bashir Ahmad, APC ce za ta lashe zabe a Kano.

Bashir Ahmad, mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin yada labarai ta yanar gizo, ya wallafa hotonsa a shafinsa na Twitter a wani filin wasa da ke Qatar yana kallonq wasan gasar cin kofin duniya.

Hoton ya janyo cece-kuce yayin da ‘yan jam’iyyar suka bayyana matakin da ya dauka a matsayin abin takaici.

Kokarin jin ta bakin Ahmad ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Tags: APCBashir AhmadkanoQatarYakin Neman Zabe
Previous Post

Asirin Namiji Mai Zamba Da Shigar Mata Ya Tonu

Next Post

An Shirya Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Matasan Sin Da Afirka Karo Na Biyu Ta Kafar Bidiyo

Related

Karancin Mai: Kungiyoyin Sufuri Za Su Yi Zanga-Zanga A Hedikwatar NNPC 
Manyan Labarai

Karancin Mai: Kungiyoyin Sufuri Za Su Yi Zanga-Zanga A Hedikwatar NNPC 

12 mins ago
Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

1 hour ago
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 
Manyan Labarai

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

2 days ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

3 days ago
Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele
Manyan Labarai

Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

3 days ago
Next Post
An Shirya Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Matasan Sin Da Afirka Karo Na Biyu Ta Kafar Bidiyo

An Shirya Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Matasan Sin Da Afirka Karo Na Biyu Ta Kafar Bidiyo

LABARAI MASU NASABA

Karancin Mai: Kungiyoyin Sufuri Za Su Yi Zanga-Zanga A Hedikwatar NNPC 

Karancin Mai: Kungiyoyin Sufuri Za Su Yi Zanga-Zanga A Hedikwatar NNPC 

February 7, 2023
Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

Yadda Aka Yi Wa ‘Yan Nijeriya 16 Kisan Gilla A Burkina Faso

February 7, 2023
Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

Tinubu Ya Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Kyautar 100m A Katsina

February 7, 2023
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Shugaban EFCC A Gidan Yarin Kuje 

February 7, 2023
Hadin Gwiwar BRICS Ya Nuna Halin Ci Gaba Mai Kyau

Hadin Gwiwar BRICS Ya Nuna Halin Ci Gaba Mai Kyau

February 7, 2023
Kotu Ta Yanke Wa Wani Tsoho Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Har Abada Kan Laifin Fyade A Jigawa

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Dakatar Da CBN Da Buhari Ƙara Wa’adin Maye Tsoffin Kuɗi

February 6, 2023
EFCC Ta Cafke Manajan Banki Kan Daukar Sabbin Kudi Da Bayar Da Su A Abuja

EFCC Ta Cafke Manajan Banki Kan Daukar Sabbin Kudi Da Bayar Da Su A Abuja

February 6, 2023
An Samar Da Damar Dawo Da Zirga-zirga A Dukkan Fannoni A Tsakanin Hong Kong Da Babban Yankin Kasar Sin

An Samar Da Damar Dawo Da Zirga-zirga A Dukkan Fannoni A Tsakanin Hong Kong Da Babban Yankin Kasar Sin

February 6, 2023
Shugaban Kasar Sin Ya Mika Sakon Jaje Ga Takwarorinsa Na Turkiyya Da Syria Bisa Ibtila’in Girgizar Kasa Da Ya Shafi Sassan Kasashen Biyu

Shugaban Kasar Sin Ya Mika Sakon Jaje Ga Takwarorinsa Na Turkiyya Da Syria Bisa Ibtila’in Girgizar Kasa Da Ya Shafi Sassan Kasashen Biyu

February 6, 2023
Tawagogin Sinawa Masu Yawon Shakatawa Sun Sake Fara Ziyara A Ketare

Tawagogin Sinawa Masu Yawon Shakatawa Sun Sake Fara Ziyara A Ketare

February 6, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.