ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Siyasa Da Masu Zabe: Wane Gauta Ne Ba Ja Ba?

by Idris Aliyu Daudawa
4 years ago
Siyasa

Masu iya magana sun ce ‘Idan maciji ya sari mutum da zarar ya ga tsumma sai ya yi tsammanin wani ne zai kara saransa wannan al’amarin haka ne yake, zuwa yanzu dai abin da ake jira shi ne zaben 2023, an yi zabubbuka samfuri biyu, na shugaban kasa, gwamnoni, majalisun dokoki na tarayya da Jihohi, kai har ma da na ‘yan autan mukaman siyasa wato Kansiloli.

Duk wani abin da dan siyasa yake yi sai ya samu hadin kai na masu yin zabe, da jagororinsu. Akwai masu tunanin watakila an yi karatun ta natsu, sai dai har yanzu abin bai canza zane ba.

  • Tsoma Baki Da Lalata Tsarin Samar Da Kayayyaki Da Amurka Ke Yi Bai Samu Karbuwa Ba
  • Sin Tana Bayar Da Damar Hadin Gwiwa Ta Hanyar Ayyukan Binciken Duniyar Wata Na Chang’e

Yayin da wasu Kansilolin gwamnonin ne suke dauki dora, wani lokacin ma har da Shugabannin kananan humomin nadi ake yi a wasu Jihohin ba zabe ba, sai dai abinda gwamna ya ga damar yi domin shi ne yake da  wuka da nama a hannunsa. .

ADVERTISEMENT

Halin da  ake ciki yanzu ku san fiye da shekara bakwai suna kan karagar mulkin, duk da yake dai ba a taru aka zama daya ba, akwai wadanda sun maida ragon Layyarsu, yayin da wasu kuma har yanzu ana bin su bashi sun kasa maidawa. Idan bera na da sata to ita ma daddawa tana da wari.

Wasu ma ‘yan siyasar bayan zaben nasu wasu ma ba a barin ko nisawa su fara yi, ko rantsar da su ba a yi ba, ko ma kanshin ita majalisar ba su fara ji ba, amma sai ka ga ana ta turereniya wani lokaci wajen zuwa ganinsu.

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

Wani abu mai daure kai shi ne yadda ranar zabe za ka ga wasu masu kada kuri’a sun sa ganye a kansu, ma’ana wadannan suna nuna cewar su a kasuwa suke, jira kawai suke a taya. Watakila ma shi ya sa Bahaushe yake cewa kowanne Gauta ja ne sai dai idan ba a kai shi rana ba amma  a cikin wasan dare, kamar yadda aka ce mugu shi ne wanda ya san makwancin mugu, tamkar dai barawon  tsaye ne da na zaune. To da zarar masu sayen kuri’u sun ga irin wadannan masu son sayar da katin zabensu abin da aka fi sani da kuri’a, wannan shi ake cewa kaya sun tsinke a gindin kaba.

Ina iya tunawa a shekarar 2015 na je Jihar Zamfara daga sashen Arewa maso yamma na ga irin wannan al’amari wanda ya yi matukar ba ni mamaki, saboda yadda masu aikata wannan al’amari na sayen kuri’a da masu sayarwa a wata mazabar da ba ta da nisa da Unguwar Zabarmawa a Gusau babban birnin Jihar suka ci karensu babu babbaka. Wani al’amari kuma mai daure kai da ban al’ajabi shi ne lokacin da ake al’adar nan ta tantancewa, wani lokacin a cikin gidan mutum za a shiga a yi mashi cin mutunci da sunan tantancewa.

A gabana na ga yadda aka fara zabga wa wani matashi bulala da sunan tantancewa kamar wadanda da ma akwai jikakka tsakaninsu. Ana yin magana ai wane ba rago ba ne zai iya shanyewa har sai da ta kai ga ba ya iya jurewa, da ya ga abin ba zai iya jurewa ba sai ya ranta a na kare. Duk irin wannan ai ‘yan barandar wasu ‘yan siyasa ne suka aiwatar da ita mummunar al’adar ta  tantancewa, da ma masu iya magana sun ce kowa ya samu rana sai ya yi shanya.

A wancan lokacin da yake talauci bai kai tsananin na yanzun ba, abin da na gane wa idanuna a wata mazaba, na ga masu sayen kurui’u, tare da masu sayarwa. Abin na nuna kowa ya san kowa, suna zuwa sai ya amshi kuri’ar ya ba su dan abinda bai taka kara ya karya ba, domin bai wuce Naira 200 ba, har wata da ta bayar da kuri’arta, aka ba ta abin hasafin nata, har ma magana take cewa yau ta samu abin yin jar miya. Wannan duk ya faru ne a gaban jam’an tsaro wadanda su dama aikinsu shi ne idan sun ga irin haka su yi saurin daukar mataki, amma ina shiru kake ji kamar an aiki bawa garinsu.

Idan har irin wannan abin takaicin zai iya faruwa a babban birnin Jiha ko na ce hedikwatar Jiha a ranar da ake zabe, me zai iya faruwa ke nan a kauyuka wuraren da ba kasafai ake samun isassun jami’an tsaro ba?

Sai kuma wata karamar hukuma a Arewa da wani al’amari ya kai ni can inda na ga wani abin da ya kara ba ni mamaki da ya fi wanda na gani da farko, domin kuwa irin ‘yan siyasar da ake kira ‘yan goma-goma irin na mazabun Kansila. Bayan sun ci abincin rana a sakatariyar karamar hukumar sai ka ga mutum yana sosa keya, kamar yaron da ya aikata laifi aka kama shi, abin da za ka ji ya ambata a matsayin bankwana sai ya ce wallahi yau ban da kudin cefane, ko zai yi ma ‘yarsa aure, kai da dai sauran abubuwan da ba su kamata ba a ce ana fada wa masu mukaman siyasa.

Dukkan wadanda suka yi bankwana da shugaban karamar hukumar babu mutumin da ya yi maganar a unguwarsu suna bukatar a zo a yi masu aikin da zai bunkasa wurin nasu. Kowa bukatar kansa yake gabatarwa kamar dai yadda na ji da kunnena, don haka a irin wannan yanayin ne har za a yi maganar wani ci gaban al’umma, ni a nawa ganin abin ai zai yi matukar wuya.

Ba abin mamaki ba ne ganin yadda wasu mutane za su yi tafiyayya daga garuruwansu babu kuma inda za su yi birki sai Majalisar Wakilai, ko ta Dattawa haka abin yake har zuwa na Jihohi duk dai Kanwar ja ce. Ko a same su a ofis ko a je gidajensu, duk dai bukatun na mutane ne inda kowa yake bayyana nasa.

Wani lokaci ma sai su manta da kwatancen hanyar da za su bi zuwa gidan sai sun tambaya, da gangan ne ma har ka saurari mutane suna maganar cewa babu wasu ayyukan da aka yi masu wadanda za su kawo masu ci gaba. Ai abin yana da  kamar wuya Gurguwa da auren nesa, saboda dama in har an hau motar kwadayi to dole  a sauka  a tsashar wulakanci.

Akwai mutanen mazabun da suke bibiyar ayyukan da za a yi masu na mazabu, da kudaden da aka ware, da kuma lokacin da za a fara yin su ayyukan. Ta daya bangarensu ba a yi ayyukan da mutanensu za su amfana ba, tambaya suke yaushe ne dan majalisar nasu zai zo ne, domin su je su bayyana ma shi nasu bukatunsu.

Ba ana nufi babu masu bibiyar lokacin da ake ba da kudaden yi wa mazabu aiki ba ne a Arewa domin ai ba a rasa nono a ruga, amma ba su kai yawan sashen kudancin Nijeriya ba. Abubuwan cin fuska da wasu ‘yan majalisun Arewa ke yi wa mazabunsu, idan Kudanci ne ba yadda za su ko ma  ko mafarki yin hakan, saboda sun san kwanan wasan.

Da yake tuni suka tsaga suka ga jinni, sun san duk yadda za su tafiyar da mutanen nasu, musamman ma idan sun lura su ba wata maganar ci gaban al’ummarsu ne ya dame su, ashe dama wasu daga cikinsu bukatarsu aljihunsu.

Muddin dai wasu  mutane suka nuna kwadayin sai sun samu abin yin hidima, lalle za a dade ana cin tuwon shekaranjiya da miyar wata daya. Shi ya sa ake kallon tsakanin `Yan Siyasa Da Masu Zabe Wane Gautan Ne Ba Ja Ba?

Siyasa
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara
Bakon Marubuci

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
Bakon Marubuci

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
Next Post
Sarkin Zazzau Ya Nada Sabon Ardon Zazzau

Sarkin Zazzau Ya Nada Sabon Ardon Zazzau

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.