ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Ministan Tsaro

by Leadership Hausa
2 days ago
Ministan

Nada Tsohon Hafsan Sojin Rundunar Tsaron Kasar nan Janar Christopher Musa mai murabus, a mukamin Babban Ministan Tsaro, hakan na kara janyo yin tsokaci, musamman a kafafen yada Labarai.

Wasu da dama na yin hasashen cewa, nadin na sa, ya zo a kan gaba musamman duba da cewa, a wannan mulkin na Demokiradiyya ne, aka fara samun nada, tsohon babban hafsan soji,a mukamin na babban ministan tsaro, kasar jim kadan bayan ya yi murabus.

  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Farfesa Ibrahim Tsafe A Matsayin Sabon Shugaban Jami’ar ZAMSUT
  • Sin: An Kaddamar Da Manufar Kafa Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta A Tsibirin Hainan

Masu ruwa da tsaki da dama, sun yi maraba da nadin wanda hakan ya nuna cewa, wani babban mataki ne, na nufin magance kalubalen rashin tsaro da kasar ke ci gaba da fuskanta.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ita ma wannan Jaridar, ta bi sahun ra’ayin wadannan masu ruwa da tsakiin wajen yin maraba da nadin na Musa musamman idan aka yi la’kari da irin kwarewa da bisirarsa, da ya samu a gidan soja.

Sai dai, wannan Jaridar na ganin wannan nadin na sa, cike yake da babban nauyi da aka dora masa wanda kuma bai da wata dama, ta gabatar da uzuri, kan wannan nauyin da zai iya bayarwa, wajen sauke nauyin.

LABARAI MASU NASABA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Mutane da dama dai, na ganin bai kamata ace. Musa ya gaza sauke wannan nauyin ba, musamman ganin cewa, a matsayin na tsohon babban hafsan soji, ya san duk wani shige da fice, da zai yi, domin kawo karshen kalubalen na rashin tsaro, da ya yiwa kasar kakatutu.

Tabbas, nauyin da ke a Kansas, ba karami bane, musamman duba da cewa, a lokacin da ‘yan majalisa ke tabtance shi a zauren majalisa, ya zayyano wasu daga cikin manyan matsalolin, da yake son ya tunkara kan matsalar ta rashin tsaro.

Matsalar daya da ya kamata Musa a yanzu ya tunkara ita ce, ta bazuwar makamai ba bisa ka’ida ba, a hannun wasu alumomin kasar, wadda kuma ake ganin ke janyo cikas na gudanar da ayyukan sojin kasar.

Kazalika, wannan Jaridar, na ganin ya kuma zama wajibi sabon babban ministan tsaron ya tabbatar da an wadata dakarun sojin kasar da kayan yaki yadda za su tunkari duk wani kalubalen rashin tsaro a kasar.

A shekarar 2024 ne dai, Nijeriya ta rattaba hannun yarjejeniyar da hukumar kera makamai ta kasa wato NASENI tare da kuma ma’aikatar tsaro ta kasa,domin a kera makamai da kuma kula da su, inda wannan Jaridar na ganin cewa, wannan mataki ne da ya dace matuka.

Bugu da kari, wani babban abin sha’awa shi ne, sabon babban ministan tsaron, a baya ya kadsncr a kan gaba wajen ssmar da dimbin dsbarun da za a bi, domin lalubo da mafita kan lamarin matsalar tsaro a kasar nan.

Hakan ne ya sanya, a lokacin da ya ke rike da mukamin na babban hafsan tsaro na soji, ya shirya taron manyan hafsoshin soji na nahiyar Afirka wanda aka gudanar a Abuja.

Taron ya samu halartar manyan hafsoshin soji guda 37, da suka fito daga nahiyar Afirka, musamman a lokacin taron sun tattauna kan yadda za a magance matsalolin rashin tsaro a tsakanin kasashen Afirka

A jawabin da ya gabatar a wajen taron, a lokacin yana rike da mukamin na babban hafsan rundunar tsaron kasar Musa ya bayyana cewa, lokacin kawo kasashen kalubalen rashin tsaro da nahiyar Afirka ke fuskanta ya zo karshe kuma dole ne, mu tashi haikan, wajen tsayawa tsayin daka, domin tunkarar matsalar ta hanyar samar da kudaden fa za a yi aiki domin bai kasashen mu, kariyar da ta kamata.

A namu ra’ayin kan wannan furucin na sabon babban ministan tsaron, tamkar umarni ne na tabbatar da an samar da wadataccen tsaro.

Kadancewar a yanzu Christopher Musa ne ke rike da mukamin na babban ministan tsaron kasar nan, hakan zai ba shi, yin amfani da karfin ikon da yake da shi wajen wanzar da wannan tsarin na sa, ba tare da bata wani lokaci ba.

Akwai bukatar a mayar da hankali a bangaren samar da tsari da kuma tabbatar da an wanzar da tsarin, ba tare bata wani lokaci ba.

Hakazalika, akwai nauyi a kan ma’aikatar tsaro wajen bayar da shawarin da sika shafi fannin gudanar da mulki da bayar da goyon baya akan lokaci wanda hakan zai bai wa rundunar sojin kasar gudanar da ayyukan ta, yadda ya kamata.

Wannan wani nauyi ne babba da aka dorawa sabon babban ministan tsaron kuma mai kunshe da sarkaiyar wandarwa.

A matsayin mu a wannan Jaridar, muna da yakin cewa, a yanzu rundunar sojin kasar a shirye take domin tunkarar duk wata barazanar rashin tsaro da kasar ke fuskanta. Fadin namu na hakan na zuwa ne, musamman dangane da irin labarukan da muke wallafawa na ci gaba a fannin tsaro na kasar nan da kuma irin fashin baki da muke yi, kan lamarun yau da kullum na kasar nan.

Babbar shawarar ga sabon babban ministan tsaron ita ce, kar ya daga kafa wajen kawo karshen kalubalen rashin tsaro a kasar, musamman duba da cewa, daukacin ‘yan kasar, sun jima da gajiya da batun na kalubalen na rashin tsaro.

Wannan Jaridar, na da kwarin guwair cewa, sabon babban ministan tsaron ba da duk wata kwarewar da ake bukata, domin sauke nauyin da aka dora masa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi
Hotuna

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Rikicin Dangote Da Dillalan Fetur Ya Dauki Sabon Salo

Rikicin Dangote Da Dillalan Fetur Ya Dauki Sabon Salo

LABARAI MASU NASABA

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.