ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jan Aikin Da Ke Gaban Sabon Babban Ministan Tsaro

by Leadership Hausa
7 months ago
Ministan

Nada Tsohon Hafsan Sojin Rundunar Tsaron Kasar nan Janar Christopher Musa mai murabus, a mukamin Babban Ministan Tsaro, hakan na kara janyo yin tsokaci, musamman a kafafen yada Labarai.

Wasu da dama na yin hasashen cewa, nadin na sa, ya zo a kan gaba musamman duba da cewa, a wannan mulkin na Demokiradiyya ne, aka fara samun nada, tsohon babban hafsan soji,a mukamin na babban ministan tsaro, kasar jim kadan bayan ya yi murabus.

  • Gwamnan Zamfara Ya Naɗa Farfesa Ibrahim Tsafe A Matsayin Sabon Shugaban Jami’ar ZAMSUT
  • Sin: An Kaddamar Da Manufar Kafa Hidimar Kwastam Mai Zaman Kanta A Tsibirin Hainan

Masu ruwa da tsaki da dama, sun yi maraba da nadin wanda hakan ya nuna cewa, wani babban mataki ne, na nufin magance kalubalen rashin tsaro da kasar ke ci gaba da fuskanta.

ADVERTISEMENT

Kazalika, ita ma wannan Jaridar, ta bi sahun ra’ayin wadannan masu ruwa da tsakiin wajen yin maraba da nadin na Musa musamman idan aka yi la’kari da irin kwarewa da bisirarsa, da ya samu a gidan soja.

Sai dai, wannan Jaridar na ganin wannan nadin na sa, cike yake da babban nauyi da aka dora masa wanda kuma bai da wata dama, ta gabatar da uzuri, kan wannan nauyin da zai iya bayarwa, wajen sauke nauyin.

LABARAI MASU NASABA

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

Mutane da dama dai, na ganin bai kamata ace. Musa ya gaza sauke wannan nauyin ba, musamman ganin cewa, a matsayin na tsohon babban hafsan soji, ya san duk wani shige da fice, da zai yi, domin kawo karshen kalubalen na rashin tsaro, da ya yiwa kasar kakatutu.

Tabbas, nauyin da ke a Kansas, ba karami bane, musamman duba da cewa, a lokacin da ‘yan majalisa ke tabtance shi a zauren majalisa, ya zayyano wasu daga cikin manyan matsalolin, da yake son ya tunkara kan matsalar ta rashin tsaro.

Matsalar daya da ya kamata Musa a yanzu ya tunkara ita ce, ta bazuwar makamai ba bisa ka’ida ba, a hannun wasu alumomin kasar, wadda kuma ake ganin ke janyo cikas na gudanar da ayyukan sojin kasar.

Kazalika, wannan Jaridar, na ganin ya kuma zama wajibi sabon babban ministan tsaron ya tabbatar da an wadata dakarun sojin kasar da kayan yaki yadda za su tunkari duk wani kalubalen rashin tsaro a kasar.

A shekarar 2024 ne dai, Nijeriya ta rattaba hannun yarjejeniyar da hukumar kera makamai ta kasa wato NASENI tare da kuma ma’aikatar tsaro ta kasa,domin a kera makamai da kuma kula da su, inda wannan Jaridar na ganin cewa, wannan mataki ne da ya dace matuka.

Bugu da kari, wani babban abin sha’awa shi ne, sabon babban ministan tsaron, a baya ya kadsncr a kan gaba wajen ssmar da dimbin dsbarun da za a bi, domin lalubo da mafita kan lamarin matsalar tsaro a kasar nan.

Hakan ne ya sanya, a lokacin da ya ke rike da mukamin na babban hafsan tsaro na soji, ya shirya taron manyan hafsoshin soji na nahiyar Afirka wanda aka gudanar a Abuja.

Taron ya samu halartar manyan hafsoshin soji guda 37, da suka fito daga nahiyar Afirka, musamman a lokacin taron sun tattauna kan yadda za a magance matsalolin rashin tsaro a tsakanin kasashen Afirka

A jawabin da ya gabatar a wajen taron, a lokacin yana rike da mukamin na babban hafsan rundunar tsaron kasar Musa ya bayyana cewa, lokacin kawo kasashen kalubalen rashin tsaro da nahiyar Afirka ke fuskanta ya zo karshe kuma dole ne, mu tashi haikan, wajen tsayawa tsayin daka, domin tunkarar matsalar ta hanyar samar da kudaden fa za a yi aiki domin bai kasashen mu, kariyar da ta kamata.

A namu ra’ayin kan wannan furucin na sabon babban ministan tsaron, tamkar umarni ne na tabbatar da an samar da wadataccen tsaro.

Kadancewar a yanzu Christopher Musa ne ke rike da mukamin na babban ministan tsaron kasar nan, hakan zai ba shi, yin amfani da karfin ikon da yake da shi wajen wanzar da wannan tsarin na sa, ba tare da bata wani lokaci ba.

Akwai bukatar a mayar da hankali a bangaren samar da tsari da kuma tabbatar da an wanzar da tsarin, ba tare bata wani lokaci ba.

Hakazalika, akwai nauyi a kan ma’aikatar tsaro wajen bayar da shawarin da sika shafi fannin gudanar da mulki da bayar da goyon baya akan lokaci wanda hakan zai bai wa rundunar sojin kasar gudanar da ayyukan ta, yadda ya kamata.

Wannan wani nauyi ne babba da aka dorawa sabon babban ministan tsaron kuma mai kunshe da sarkaiyar wandarwa.

A matsayin mu a wannan Jaridar, muna da yakin cewa, a yanzu rundunar sojin kasar a shirye take domin tunkarar duk wata barazanar rashin tsaro da kasar ke fuskanta. Fadin namu na hakan na zuwa ne, musamman dangane da irin labarukan da muke wallafawa na ci gaba a fannin tsaro na kasar nan da kuma irin fashin baki da muke yi, kan lamarun yau da kullum na kasar nan.

Babbar shawarar ga sabon babban ministan tsaron ita ce, kar ya daga kafa wajen kawo karshen kalubalen rashin tsaro a kasar, musamman duba da cewa, daukacin ‘yan kasar, sun jima da gajiya da batun na kalubalen na rashin tsaro.

Wannan Jaridar, na da kwarin guwair cewa, sabon babban ministan tsaron ba da duk wata kwarewar da ake bukata, domin sauke nauyin da aka dora masa.

Ministan
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark
Manyan Labarai

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026
Next Post
Rikicin Dangote Da Dillalan Fetur Ya Dauki Sabon Salo

Rikicin Dangote Da Dillalan Fetur Ya Dauki Sabon Salo

LABARAI MASU NASABA

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026
Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Jiragen Kasan Sin Sun Yi Tafiye-Tafiyen Fasinjoji Sama Da Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

Kotu Ta Hana INEC Amincewa Da Tarukan ADC Ƙarƙashin Jagorancin David Mark

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.