• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin ‘Yan Wasan Kungiya Daya Da Suka Yi Fada Da Juna

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Jerin ‘Yan Wasan Kungiya Daya Da Suka Yi Fada Da Juna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A satin daya gabata ne dan wasa Sadio Mane da Leroy Sane suka yi fada a dakin hutun ‘yan wasa, bayan tashi daga Champions League, kamar yadda wasu jaridu suka wallafa.

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ce ta doke Bayern Munich 3-0 a wasan farko zagayen kuarter finals a gasar zakarun Turai a Etihad kuma ‘yan wasan biyu sun bai wa hammata iska, bayan tashi daga karawar har sai da aka shiga tsakaninsu.

  • Nijeriya Ta Sanya Hannu A Yarjejeniyar Amfani Da Fasahar Shuka Itatuwa Da Kasar Netherlands
  • Me Ya Sa Karin Kamfanonin Ketare Suka Samu Ra’ayin Bai Daya Kan Zuwa Kasar Sin Don Raya Kansu?

Rahotanni sun bayyana cewa Mane ya naushi Sane tsohon dan kwallon Manchester City a fuska, har lebensa ya dan tsage sai dai ba wannan ne karon farko da aka yi fada tsakanin ‘yan kungiya daya ba, ko dai a wajen atisaye har a filin wasa ko bayan an kammala gasa.

Tuni kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen ta dakatar da dan wasa Sadio Mane daga buga mata wasa ranar Asabar din da ta gabata, ta kuma ce za ta hukunta shi bisa abinda ya faru.

-Ga jerin wasu daga fadan da aka yi tsakanin ‘yan kungiya daya:-

Labarai Masu Nasaba

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Ibrahimobic da Onyewu

Dan wasa Zlatan Ibrahimobic ya yi kaurin suna wajen fada da abokan wasansa, domin ya taba yi wa Rafael ban der Baart barazanar zai karya masa kafa a Ajad ya kuma naushi Jonathan Zebina a fuska a Jubentus.

To sai dai wanda ya fi muni shi ne wanda ya yi a kungiyar kwallon kafa ta AC Milan, inda ya yi fada da Oguchi Onyewu, wanda ke buga wasa aro a Newcastle United daga kungiyar Italiya.

Batty da Le Saud

Blackburn Robers ta kasa taka rawar gani a Champions League, bayan lashe Premier League a lokacin ta ziyarci Spartak Moscow a wasa na biyar a cikin rukuni, bayan kasa yin nasara a fafatawar biyar.

A Rashan an ci Blackburn 3-0 a wasan ne Dabid Batty da Graeme Le Saud suka dunga dukan juna da kyar aka raba su. Drinkwater da Jota Ba za ka taba cewa ‘yan wasan da suka yi zaman benci za su bai wa hammata iska ba, abin da ya faru tsakanin Drink Water da Jota kenan a wajen atisaye, kwana daya tsakani da Aston Billa ta ci Leicester City 4-0 – ‘yan wasan Leicester da ba su buga karawar ba na atisaye a Bodymoor Hearth – sai cece kuce ya barke tsakanin Drinkwater da Jota, inda ‘yan wasan Ingila suka yi wa kansu gware, sai da aka shiga tsakaninsu.

Lloris da Son Tottenham ta yi nasara a kan kungiyar kwallon Eberton da cin 1-0 a watan Yulin shekara ta 2020, amma batun da ya fi jan hankali bayan hutu shi ne rigima tsakanin Gugo Lloris da Son Heung-min.

Mai tsaron ragar Tottenham ya tuhumi Son da kin dawowa ya tare kwallo, daga baya suka barke da kokawa har sai da Giobani Lo Celso da Harry Winks suka shiga tsakani, da aka tashi daga wasan sun rungumi juna, sannan bayan tashi daga wasan kociyan kungiyar, Jose Mourinho ya ce abin da ya faru abin ban sha’awa ne.

Mitrobic da Kamara

Aleksandar Mitrobic da Aboubakar Kamara sun dambata a tsakaninsu, bayan da Kamara ya karbe kwallo daga hannun dan Serbia suna Fulham ya buga fenariti a karawa da Huddersfield – akuma bi ci ba.

Adebayor da Bendtner

Emmanuel Adebayor shima daya daga ‘yan wasan da ke fada da abokan wasansa ne, sun bai wa hammata iska da Kolo Toure a Manchester City a

lokacin atisaye a 2011 sai dai tun kafin wannan, Adebayo ya yi fada da Nicklas Bendtner a Arsenal a 2008, wanda aka ce ya yi wa dan kasar Denmark gware a wasan da Tottenham ta ci 5-1 a League Cup wasan daf da karshe.

Robben da Ribery

Za’a iya cewa abin mamaki idan aka ce an yi fada tsakanin Arjen Rubben da Frank Ribery a lokacin gasar zakarun turai na Champions League

tsakanin Bayern Munich da Real Madrid. ‘Yan wasan guda biyu sun yi takaddama kan wanda zai yi bugun tazara, an yi zargin Ribery ya naushi Robben, amma Bayern ba ta ce komai kan lamarin kuma har yanzu babu wata magana daga kungiyar.

Shearer da Gillespie

An yi wani kazamin rikici tsakanin Alan Shearer wanda ta kai sai da aka dangana da Keith Gillespie zuwa asibiti ‘yan wasan Newcastle United a kakar wasa ta shekarar 1997.

Lehmann da Amoroso

Daman dai an bayyana cewa Jens Lehmann ba shi da hakuri ko kadan, ya kuma kalubalanci Marcio Amoroso, bayan da kungiyar Schalke ta zura kwallo a kungiyar su Borussia Dortmund a 2003.

An bai wa mai tsaron raga Lehman jan kati a karawar, wanda ya zama mai tsaron raga na farko a Bundesliga mai wannan tarihin da aka kora karo na hudu – daga baya aka soke kwallon da cewar akwai satar gida – inda suka tashi canjaras.

Ljungberg da Mellberg Mare-mare aka yi tsakanin Freddie Ljungberg da Olof Mellberg, wanda hakan ya ja hankalin manema labarai a lokacin da ake shirin zuwa gasar kofin duniya a kasashen Korea da Japan a 2002.

Ricksen da Radimob

Rahotanni sun bayyana cewa Fernando Ricksen mafadaci ne, wanda ya yi rigima da kyaftin, Bladislab wata daya da komawarsa Zenit sai dai tun kafin nan ya yi rigima da Malaga a lokacin atisaye.

Za’a iya cewa fadan da aka yi tsakanin ‘yan kungiya daya a tarihi yana da yawa da aka yi a baya, za kuma a ci gaba da yi duk da matakan ladabtarwa da kungiyoyi ke dauka a kan ‘yan wasan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaFada Da junaKwallon Kafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilan Da Suka Sa Messi Ya Shiga Jerin Mutum 100 Masu Daraja A Duniya

Next Post

Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe

Related

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
Wasanni

Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau

3 days ago
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 
Wasanni

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

4 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 days ago
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro
Wasanni

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

6 days ago
PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 
Wasanni

PSG Ta Yi Waje Rod Da Arsenal A Gasar Zakarun Turai 

1 week ago
UEFA: Inter Milan Ta Yi Wa Barcelona Kancal
Wasanni

UEFA: An Kai Ruwa Rana Yayin Da Inter Ta Koro Barcelona Gida

1 week ago
Next Post
Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe

Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.