• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin ‘Yan Wasan Kungiya Daya Da Suka Yi Fada Da Juna

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
in Wasanni
0
Jerin ‘Yan Wasan Kungiya Daya Da Suka Yi Fada Da Juna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A satin daya gabata ne dan wasa Sadio Mane da Leroy Sane suka yi fada a dakin hutun ‘yan wasa, bayan tashi daga Champions League, kamar yadda wasu jaridu suka wallafa.

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ce ta doke Bayern Munich 3-0 a wasan farko zagayen kuarter finals a gasar zakarun Turai a Etihad kuma ‘yan wasan biyu sun bai wa hammata iska, bayan tashi daga karawar har sai da aka shiga tsakaninsu.

  • Nijeriya Ta Sanya Hannu A Yarjejeniyar Amfani Da Fasahar Shuka Itatuwa Da Kasar Netherlands
  • Me Ya Sa Karin Kamfanonin Ketare Suka Samu Ra’ayin Bai Daya Kan Zuwa Kasar Sin Don Raya Kansu?

Rahotanni sun bayyana cewa Mane ya naushi Sane tsohon dan kwallon Manchester City a fuska, har lebensa ya dan tsage sai dai ba wannan ne karon farko da aka yi fada tsakanin ‘yan kungiya daya ba, ko dai a wajen atisaye har a filin wasa ko bayan an kammala gasa.

Tuni kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen ta dakatar da dan wasa Sadio Mane daga buga mata wasa ranar Asabar din da ta gabata, ta kuma ce za ta hukunta shi bisa abinda ya faru.

-Ga jerin wasu daga fadan da aka yi tsakanin ‘yan kungiya daya:-

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Ibrahimobic da Onyewu

Dan wasa Zlatan Ibrahimobic ya yi kaurin suna wajen fada da abokan wasansa, domin ya taba yi wa Rafael ban der Baart barazanar zai karya masa kafa a Ajad ya kuma naushi Jonathan Zebina a fuska a Jubentus.

To sai dai wanda ya fi muni shi ne wanda ya yi a kungiyar kwallon kafa ta AC Milan, inda ya yi fada da Oguchi Onyewu, wanda ke buga wasa aro a Newcastle United daga kungiyar Italiya.

Batty da Le Saud

Blackburn Robers ta kasa taka rawar gani a Champions League, bayan lashe Premier League a lokacin ta ziyarci Spartak Moscow a wasa na biyar a cikin rukuni, bayan kasa yin nasara a fafatawar biyar.

A Rashan an ci Blackburn 3-0 a wasan ne Dabid Batty da Graeme Le Saud suka dunga dukan juna da kyar aka raba su. Drinkwater da Jota Ba za ka taba cewa ‘yan wasan da suka yi zaman benci za su bai wa hammata iska ba, abin da ya faru tsakanin Drink Water da Jota kenan a wajen atisaye, kwana daya tsakani da Aston Billa ta ci Leicester City 4-0 – ‘yan wasan Leicester da ba su buga karawar ba na atisaye a Bodymoor Hearth – sai cece kuce ya barke tsakanin Drinkwater da Jota, inda ‘yan wasan Ingila suka yi wa kansu gware, sai da aka shiga tsakaninsu.

Lloris da Son Tottenham ta yi nasara a kan kungiyar kwallon Eberton da cin 1-0 a watan Yulin shekara ta 2020, amma batun da ya fi jan hankali bayan hutu shi ne rigima tsakanin Gugo Lloris da Son Heung-min.

Mai tsaron ragar Tottenham ya tuhumi Son da kin dawowa ya tare kwallo, daga baya suka barke da kokawa har sai da Giobani Lo Celso da Harry Winks suka shiga tsakani, da aka tashi daga wasan sun rungumi juna, sannan bayan tashi daga wasan kociyan kungiyar, Jose Mourinho ya ce abin da ya faru abin ban sha’awa ne.

Mitrobic da Kamara

Aleksandar Mitrobic da Aboubakar Kamara sun dambata a tsakaninsu, bayan da Kamara ya karbe kwallo daga hannun dan Serbia suna Fulham ya buga fenariti a karawa da Huddersfield – akuma bi ci ba.

Adebayor da Bendtner

Emmanuel Adebayor shima daya daga ‘yan wasan da ke fada da abokan wasansa ne, sun bai wa hammata iska da Kolo Toure a Manchester City a

lokacin atisaye a 2011 sai dai tun kafin wannan, Adebayo ya yi fada da Nicklas Bendtner a Arsenal a 2008, wanda aka ce ya yi wa dan kasar Denmark gware a wasan da Tottenham ta ci 5-1 a League Cup wasan daf da karshe.

Robben da Ribery

Za’a iya cewa abin mamaki idan aka ce an yi fada tsakanin Arjen Rubben da Frank Ribery a lokacin gasar zakarun turai na Champions League

tsakanin Bayern Munich da Real Madrid. ‘Yan wasan guda biyu sun yi takaddama kan wanda zai yi bugun tazara, an yi zargin Ribery ya naushi Robben, amma Bayern ba ta ce komai kan lamarin kuma har yanzu babu wata magana daga kungiyar.

Shearer da Gillespie

An yi wani kazamin rikici tsakanin Alan Shearer wanda ta kai sai da aka dangana da Keith Gillespie zuwa asibiti ‘yan wasan Newcastle United a kakar wasa ta shekarar 1997.

Lehmann da Amoroso

Daman dai an bayyana cewa Jens Lehmann ba shi da hakuri ko kadan, ya kuma kalubalanci Marcio Amoroso, bayan da kungiyar Schalke ta zura kwallo a kungiyar su Borussia Dortmund a 2003.

An bai wa mai tsaron raga Lehman jan kati a karawar, wanda ya zama mai tsaron raga na farko a Bundesliga mai wannan tarihin da aka kora karo na hudu – daga baya aka soke kwallon da cewar akwai satar gida – inda suka tashi canjaras.

Ljungberg da Mellberg Mare-mare aka yi tsakanin Freddie Ljungberg da Olof Mellberg, wanda hakan ya ja hankalin manema labarai a lokacin da ake shirin zuwa gasar kofin duniya a kasashen Korea da Japan a 2002.

Ricksen da Radimob

Rahotanni sun bayyana cewa Fernando Ricksen mafadaci ne, wanda ya yi rigima da kyaftin, Bladislab wata daya da komawarsa Zenit sai dai tun kafin nan ya yi rigima da Malaga a lokacin atisaye.

Za’a iya cewa fadan da aka yi tsakanin ‘yan kungiya daya a tarihi yana da yawa da aka yi a baya, za kuma a ci gaba da yi duk da matakan ladabtarwa da kungiyoyi ke dauka a kan ‘yan wasan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan WasaFada Da junaKwallon Kafa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dalilan Da Suka Sa Messi Ya Shiga Jerin Mutum 100 Masu Daraja A Duniya

Next Post

Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe

Related

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida
Wasanni

Gwamna Aiyedatiwa Ya Bai wa Ƴar Super Falcons Tosin Demehin ₦30m Da Gida

19 hours ago
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace
Wasanni

Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

1 day ago
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?
Wasanni

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

3 days ago
Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray
Wasanni

Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray

5 days ago
Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
Wasanni

Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta

6 days ago
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
Wasanni

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

6 days ago
Next Post
Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe

Yadda Manyan Jam’iyyu Suka Fada Cikin Rikici Bayan Zabe

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

Kasar Sin Ta Sanar Da Matakan Fara Bayar Da Ilimin Kafin Firamare Kyauta

August 5, 2025
Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

Shugaban IWGA: Birnin Chengdu Zai Karbi Bakuncin Gasar Wasanni Mafi Kyau A Tarihi

August 5, 2025
Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

Jigawa Ta Fitar Da ₦1.5bn Na Lamunin Noma Ga Ma’aikatan Gwamnati Kashi Na Biyu

August 5, 2025
Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

Matakin Baiwa Kansa Hakuri Ba Zai Kawar Da Matsayin Gwamnatin Lai Ching-te Na Kasancewa ’Yar Dara A Hannun Amurka Ba

August 5, 2025
Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

Sin Ta Fitar Da Shirin Kyautata Muhalli Domin Inganta Kiwon Lafiya Na Shekaru Biyar

August 5, 2025
Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

Ruftawar Gini Ya Kashe Uwa Da ‘Ya’yanta Biyar A Katsina

August 5, 2025
Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

Sashen Cinikayyar Samar Da Hidimomi Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso Takwas A Rabin Farko Na Shekarar 2025

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.