• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Gombe Ta Rusa Kamfanin Zuba Jari Da Bunƙasa Ƙadarori

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai, Siyasa
0
Jihar Gombe Ta Rusa Kamfanin Zuba Jari Da Bunƙasa Ƙadarori
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Zartarwar Jihar Gombe ƙarƙashin jagorancin Gwamna Mahammadu Inuwa Yahaya ta amince da rusa Kamfanin Zuba Jari da Bunƙasa ƙadarori na Jihar Gombe, GIPDC. 

Kwamishinan kuɗi da bunƙasa tattalin arziƙi, Malam Muhammadu Gambo Magaji, ne ya sanar da hakan, yana mai cewa an ɗauki matakin ne don daidaitawa da ƙarfafa hukumomin zuba jari na jihar.

“Bayan nasarar da aka samu a babban taron zuba jari na Gombe na 2022 da kuma burinmu na karɓar baƙuncin wani taron na gaba da za a yi a watan Oktobar bana, tare da ci gaba da riƙe kambunmu na jagora a fagen sauƙaƙa kasuwanci, gwamnati ta ɗauki wani tsari mai inganci na ƙarfafa hukumomin zuba jari da kuma magance kashe-kashen kuɗaɗe ba gaira ba dalili da ma kawo ƙarshen maimaita ayyuka”

  • Ƴansandan Gombe Sun Yi Ram Da Ɓarayin Hanyar Jirgin Ƙasa
  • ‘Yansanda Sun Cafke Kansila Da Hakimi Kan Zargin Satar Taransifoma A Gombe

Kwamishinan ya ƙara da cewa, “Duba da yadda Kamfanin Zuba Jari da Bunƙasa Kadarorin na Jihar Gombe da Kamfanin Haɓaka Kuɗaɗen Shiga na jihar suke aiki iri ɗaya, majalisar zartarwar ta yanke shawarar rushe kamfanin zuba jari da bunƙasa kadarorin na jiha (GIPDC) da nufin daidaita ayyukansa da rage kashe-kashen kuɗi dama inganta aiki”.

Ya ce za a mayar da ayyukan kamfanin zuwa wasu hukumomin da abin ya shafa, “Kamfanin Haɓaka kuɗaɗen shiga da bunƙasa kadarorin zai koma GROCOL, sannan za a mayar da ɓangaren bunƙasa gidaje ga Ma’aikatar Gidaje ta Jihar Gombe, kuma nan ba da daɗewa ba Gwamna zai naɗa shugabannin da za su jagoranci hukumar, za a mayar da harkokin kasuwanci da zuba jarin da GIPDC ke da su ga kamfanin Gombe State Security Company Ltd da ya zama kufai”

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Hon. Gambo Magaji ya jaddada cewa matakin ba zai shafi ma’aikatan kamfanin ba ta kowace fuska, yana mai cewa za a sake fasalin hukumar gudanarwar ta yadda za a samu sauƙin gudanar da ayyuka masu inganci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GombeTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Karkatar Da Goron Sallah: Ku Dawo Da Kuɗin Ma’aikata Ko Mu Hukunta Ku” – Gwamnan Sakkwato

Next Post

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Nanata Bukatar Karfafa Jingar Kare Ambaliya Yayin Da Ake Kokarin Takaita Aukuwar Ambaliya A Kasar

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

25 minutes ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

2 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

4 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

7 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

9 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

10 hours ago
Next Post
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Nanata Bukatar Karfafa Jingar Kare Ambaliya Yayin Da Ake Kokarin Takaita Aukuwar Ambaliya A Kasar

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Nanata Bukatar Karfafa Jingar Kare Ambaliya Yayin Da Ake Kokarin Takaita Aukuwar Ambaliya A Kasar

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.