• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ka Kalli Kanka Ka Ga Ka Fi Karfin Bukatunka Babbar Nasara Ce – Khadija Abdullahi

by Bilkisu Tijjani
10 months ago
in Adon Gari
0
Ka Kalli Kanka Ka Ga Ka Fi Karfin Bukatunka Babbar Nasara Ce – Khadija Abdullahi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zamani a yanzu ya zo da canje-canje musamman yadda kasarmu ke yin tafiyar hawainiya ta fuskar tattalin arziki, hakan ya sanya a halin yanzu sana’o’i ana tafiya kafada da kafada tsakanin maza da mata.

KHADIJA ABBDULLAHI matashiya ce wacce ta shawarci mata kan su kama sana’a domin dogaro da kansu domin biya wa kansu bukata a wannan zamani da kowa ta kansa yake yi. Khadija ta bayyana hakan ne a tattaunawarsu da wakiliyarmu BILKISU TIJJANI ALKASSIM. Ga dai yadda hirar ta kasance:

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki…

Suna na Khadija Abdullahi Muhammad iyaye na haifaffiyar Hadeja ce Jihar Jigawa, ni an haife ni a Garin Kano na yi makaranta a Kano wannan shi ne takaitaccan tarihina.

Shin Khadija matar aure ce?

Labarai Masu Nasaba

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

A’a ni ba matar aure bace, amma dai ana niyya in sha Allahu.

Malama Khadija ‘yar kasuwa ce ko kuma ma’aikaciya ce?

Eh to ina taba kasuwanci dai kadan-kadan saboda yanzu sai a hankali wallahi mutane ba kudi a hannunsu ana dai kasuwancin Alhamdu lillah.

Wanne irin kasuwanci kike yi? 

Ina saida atamfofi da leshi da kayan kicin da takalma da jakankuna.

Me yaja hankalinki har kika shiga wannan kasuwancin?

Eh to abin da ya ja hankalina har na shiga wannan kasuwancin ni mutum ce mai son na ganni da kudi a hannuna ba na son zama babu kudi ko ban kashe ba ni dai na gan su ina jin dadi.

Mene ne matakin karatunki?

Ina da (NCE).

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

Akwai kalubale kala-kala ta wajan idan mutum ya sayi kaya ko ya ce zai turo kudi ka bashi kaya daga baya kuma kudi ya zo ya zama bai fito ba, to wannan duk suna daya daga cikin irin kalubale da muke fuskanta.

Zuwa yanzu wadan ne irin nasarori kika cimma?

Alhamdu lillah mun cimma nasarori daban-daban ka kalli kanka ka ga ka fi karfin bukatunka ma wannan babbar nasara ce Alhamdu lillah.

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Idan na duba na ga na fi karfin bukatuna har zan iya taimakawa wani to Alhamdu lillah ina jin dadi.

Ta wacce hanya kike bi wajen tallata sana’arki?

Ta kafofin sada zumunta wato social media Facebook, Instagram, Whatsapp

Da me kike so mutane su rika tunawa da ke?

Ta halaye masu kyau.

Ga karatu, ga kuma hidimomin sana’a, shin ta yaya kike samun damar gudanar da hutunki?

Eh to gaskiya lokacin da na fara sana’a na kammala karatu na gaskiya ban samu wani kalubale ba ta wannan fannin ban hada karatu da sana’a ba sai da na gama karatu na fara sana’a.

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Ina so na ji an yi min addu’ar fatan alkhairi ina jin dadi sosai.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Na samu goyon baya dari bisa dari gaskiya babu abin da za mu ce daidai Alhamdu lillah.

Kawaye fa?

Gaskiya na samu goyon bayan kawaye na sosai suna taya ni tallata kayana kuma suma suna saya.

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Ni gaskiya kwalliya ba ta dame ni ba, kayan sawa ina son abaya da duguwar rigar atamfa su ne kayan da na fi sawa.

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Shawarar da zan ba wa ‘yan uwana mata ita ce a rike sana’a, dogaro da kai, Allah ya rufa mana asiri baki daya na gode.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Adon GariKhadija
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ta Kashe Mijinta Tare Da Babbaka Gawar A Abuja

Next Post

Rashin Ilimin Iyaye Na Haifar Da Karuwar Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta (2)

Related

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure
Adon Gari

Wasu Kyawawan Ɗabi’u Da Suke Ƙarfafa Zamantakewar Aure

3 weeks ago
Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Ake Nagartaccen Tsumi?

1 month ago
Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi
Adon Gari

Mata Mu Tsaya Da Kafafunmu Kar Mu Tsaya Sai An Bamu – Khadeejah Abdullahi

4 months ago
Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar
Adon Gari

Mata Mu Dage Da Neman Ilimi Da Neman Na Kanmu -Hassana Umar

4 months ago
Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam
Adon Gari

Mata Ku Dage Da Karatu Domin Tallafa Wa Rayuwarku Da Ta ‘Ya’yanku – Zahra’u Adam

6 months ago
Nijeriya Da Brazil Sun Cimma Yarjejeniyar Bunkasa Noman Zamani A Kasar Nan
Adon Gari

Halima Aliko Dangote Ta Nemi A Ba Mata Damar Shiga Harkokin Kasuwanci Yadda Ya Kamata

6 months ago
Next Post
Rashin Ilimin Iyaye Na Haifar Da Karuwar Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta (2)

Rashin Ilimin Iyaye Na Haifar Da Karuwar Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta (2)

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.