ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ka Kalli Kanka Ka Ga Ka Fi Karfin Bukatunka Babbar Nasara Ce – Khadija Abdullahi

by Bilkisu Tijjani
2 years ago
Kalli

Zamani a yanzu ya zo da canje-canje musamman yadda kasarmu ke yin tafiyar hawainiya ta fuskar tattalin arziki, hakan ya sanya a halin yanzu sana’o’i ana tafiya kafada da kafada tsakanin maza da mata.

KHADIJA ABBDULLAHI matashiya ce wacce ta shawarci mata kan su kama sana’a domin dogaro da kansu domin biya wa kansu bukata a wannan zamani da kowa ta kansa yake yi. Khadija ta bayyana hakan ne a tattaunawarsu da wakiliyarmu BILKISU TIJJANI ALKASSIM. Ga dai yadda hirar ta kasance:

Da fari za mu so sanin cikakken sunanki da tarihinki…

ADVERTISEMENT

Suna na Khadija Abdullahi Muhammad iyaye na haifaffiyar Hadeja ce Jihar Jigawa, ni an haife ni a Garin Kano na yi makaranta a Kano wannan shi ne takaitaccan tarihina.

Shin Khadija matar aure ce?

LABARAI MASU NASABA

Sirrin Mallakar Miji 

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

A’a ni ba matar aure bace, amma dai ana niyya in sha Allahu.

Malama Khadija ‘yar kasuwa ce ko kuma ma’aikaciya ce?

Eh to ina taba kasuwanci dai kadan-kadan saboda yanzu sai a hankali wallahi mutane ba kudi a hannunsu ana dai kasuwancin Alhamdu lillah.

Wanne irin kasuwanci kike yi? 

Ina saida atamfofi da leshi da kayan kicin da takalma da jakankuna.

Me yaja hankalinki har kika shiga wannan kasuwancin?

Eh to abin da ya ja hankalina har na shiga wannan kasuwancin ni mutum ce mai son na ganni da kudi a hannuna ba na son zama babu kudi ko ban kashe ba ni dai na gan su ina jin dadi.

Mene ne matakin karatunki?

Ina da (NCE).

Wanne irin kalubale kika taba fuskanta a cikin sana’arki?

Akwai kalubale kala-kala ta wajan idan mutum ya sayi kaya ko ya ce zai turo kudi ka bashi kaya daga baya kuma kudi ya zo ya zama bai fito ba, to wannan duk suna daya daga cikin irin kalubale da muke fuskanta.

Zuwa yanzu wadan ne irin nasarori kika cimma?

Alhamdu lillah mun cimma nasarori daban-daban ka kalli kanka ka ga ka fi karfin bukatunka ma wannan babbar nasara ce Alhamdu lillah.

Wanne abu ne ya fi faranta miki rai game da sana’arki?

Idan na duba na ga na fi karfin bukatuna har zan iya taimakawa wani to Alhamdu lillah ina jin dadi.

Ta wacce hanya kike bi wajen tallata sana’arki?

Ta kafofin sada zumunta wato social media Facebook, Instagram, Whatsapp

Da me kike so mutane su rika tunawa da ke?

Ta halaye masu kyau.

Ga karatu, ga kuma hidimomin sana’a, shin ta yaya kike samun damar gudanar da hutunki?

Eh to gaskiya lokacin da na fara sana’a na kammala karatu na gaskiya ban samu wani kalubale ba ta wannan fannin ban hada karatu da sana’a ba sai da na gama karatu na fara sana’a.

Wace irin addu’a ce idan aka yi miki kike jin dadi?

Ina so na ji an yi min addu’ar fatan alkhairi ina jin dadi sosai.

Wanne irin goyon baya kike samu daga wajen iyaye da ‘yan uwanki?

Na samu goyon baya dari bisa dari gaskiya babu abin da za mu ce daidai Alhamdu lillah.

Kawaye fa?

Gaskiya na samu goyon bayan kawaye na sosai suna taya ni tallata kayana kuma suma suna saya.

Me kika fi so cikin kayan sawa da kayan kwalliya?

Ni gaskiya kwalliya ba ta dame ni ba, kayan sawa ina son abaya da duguwar rigar atamfa su ne kayan da na fi sawa.

A karshe wanne irin shawara za ki ba ‘yan uwanki mata?

Shawarar da zan ba wa ‘yan uwana mata ita ce a rike sana’a, dogaro da kai, Allah ya rufa mana asiri baki daya na gode.

Kalli
Bilkisu Tijjani
+ postsBio
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Muhimmancin Shan Ruwa Ga Kyawun Fata
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)
  • Bilkisu Tijjani
    https://hausa.leadership.ng/author/bilkisu-tijjani/
    Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

MASU ALAKA

Sirrin Mallakar Miji 
Adon Gari

Sirrin Mallakar Miji 

January 25, 2026
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
Adon Gari

Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

October 12, 2025
Next Post
Rashin Ilimin Iyaye Na Haifar Da Karuwar Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta (2)

Rashin Ilimin Iyaye Na Haifar Da Karuwar Yaran Da Ba Su Zuwa Makaranta (2)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.