• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kallo Ya Koma Kano: Gwamna Abba Na Shirin Rattaba Hannu Kan Sabuwar Dokar Masarautar Kano

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Kallo Ya Koma Kano: Gwamna Abba Na Shirin Rattaba Hannu Kan Sabuwar Dokar Masarautar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abba Kabir Yusuf, na shirin rattaba hannu kan dokar majalisar masarautu da aka yi wa kwaskwarima yayin da majalisar dokokin Jihar Kano ke ci gaba da zama a yau domin kammala dokar.

Tun a jiya ne dai jami’an tsaro suka warwatsu a duk muhimman wurare na zauren majalisar lokacin da ƙudirin dokar da ke da nufin soke kafa masarautu biyar ya tsallake karatu na farko.

  • Sanata Barau Jibrin Ya Ƙaddamar Da Motocin Zirga-Zirga A Kano
  • Majalisar Dokokin Kano Za Ta Yi Wa Dokar Da Ta Tsige Sarki Sanusi II Kwaskwarima

Shugaban masu rinjaye Lawan Hussaini Chediyar Yan Gurasa ne, ya fara miƙa buƙatar yi wa dokar masarautun Kano (gyara mai lamba 2) ta 2024, manyan sauyin da ake niyyar yi zai jirkita tsarin masarautun da tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi a shekarar 2019.

Tsohuwar dokar ta 2019 wacce ta samar da sabbin masarautun Bichi da Rano da Gaya da Ƙaraye tare da (birnin) Kano, an yi gyare-gyare da dama a cikinta, inda aka yi  kwaskwarima a baya-bayan nan a shekarar 2020 da kuma 2023.

Sashe na 3(1) na dokar ya zayyana ikon waɗannan masarautun, inda kowannensu ke da ƙananan hukumomi da dama a ƙarƙashinsu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

Garan da aka yi a shekarar 2020 biyo bayan sauke Sarki Muhammadu Sanusi II, inda aka sake fasalin majalisar ta zama Sarkin Kano a matsayin mai jan ragamar na dindindin ga ragowar masarautun.

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero
Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

Har ila yau, dokar ta bai wa gwamna, idan har majalisar Sarakunan ta amince, ya iya tsigewa ko naÉ—a sabon Sarkin a duk masarautun.

Yanzu haka dai garin Kano yayi jim a daidai lokacin da majalisar ke shirin yin zama na musamman domin amincewa da gyaran.

Daily Trust ta rawaito cewa; wani babban jami’i a majalisar dokokin ya jaddada cewa babu wani da zai iya dakatar da yin gyaran domin sun ƙuduri niyyar yin shi tuntuni, wanda hakan ke nuni da cewa an daɗe ana shirin yin garambawul ga tsarin masarautun.

Sai dai shugaban marasa rinjaye Abdul Labaran Madari, ya tabbatar da cewa duk da cewa ƴaƴan jam’iyyar APC ba sa adawa da gyaran da aka yi niyyar aiwatarwa, amma sun dage cewa ba za a rusa ko ɗaya daga cikin masarautu biyar ɗin ba, kuma Sarkin (birnin) Kano na yanzu, Aminu Ado Bayero shi zai ci gaba da zama a kan kujerarsa.

Rahotanni sun bayyana cewa Sarkin Kano da Sarkin Bichi duk ba sa gari, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce kan illar rashin nasu.

Majiyoyi na nuni da cewa da zarar majalisar ta zartar da ƙudirin, nan take Gwamna Abba Kabir Yusuf zai sanya mata hannu, wanda hakan wataƙila zai iya maido da Sarki Sanusi II.

Sarki Muhammadu Sunusi II
Sarki Muhammadu Sunusi II

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Kabir YusufAminu AdokanoMasarautun KanoSanusi Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Halarci Bikin Rantsar Da Mahamat Deby A Chadi

Next Post

Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

6 minutes ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

3 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

11 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

17 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Sarkin Shuwaka Na Kanam A Filato

20 hours ago
Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
Manyan Labarai

Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja

21 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan DimokuraÉ—iyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da ÆŠumi-É—umi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.