• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kallo Ya Koma Kano: Gwamna Abba Na Shirin Rattaba Hannu Kan Sabuwar Dokar Masarautar Kano

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Kallo Ya Koma Kano: Gwamna Abba Na Shirin Rattaba Hannu Kan Sabuwar Dokar Masarautar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abba Kabir Yusuf, na shirin rattaba hannu kan dokar majalisar masarautu da aka yi wa kwaskwarima yayin da majalisar dokokin Jihar Kano ke ci gaba da zama a yau domin kammala dokar.

Tun a jiya ne dai jami’an tsaro suka warwatsu a duk muhimman wurare na zauren majalisar lokacin da ƙudirin dokar da ke da nufin soke kafa masarautu biyar ya tsallake karatu na farko.

  • Sanata Barau Jibrin Ya Ƙaddamar Da Motocin Zirga-Zirga A Kano
  • Majalisar Dokokin Kano Za Ta Yi Wa Dokar Da Ta Tsige Sarki Sanusi II Kwaskwarima

Shugaban masu rinjaye Lawan Hussaini Chediyar Yan Gurasa ne, ya fara miƙa buƙatar yi wa dokar masarautun Kano (gyara mai lamba 2) ta 2024, manyan sauyin da ake niyyar yi zai jirkita tsarin masarautun da tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi a shekarar 2019.

Tsohuwar dokar ta 2019 wacce ta samar da sabbin masarautun Bichi da Rano da Gaya da Ƙaraye tare da (birnin) Kano, an yi gyare-gyare da dama a cikinta, inda aka yi  kwaskwarima a baya-bayan nan a shekarar 2020 da kuma 2023.

Sashe na 3(1) na dokar ya zayyana ikon waɗannan masarautun, inda kowannensu ke da ƙananan hukumomi da dama a ƙarƙashinsu.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Garan da aka yi a shekarar 2020 biyo bayan sauke Sarki Muhammadu Sanusi II, inda aka sake fasalin majalisar ta zama Sarkin Kano a matsayin mai jan ragamar na dindindin ga ragowar masarautun.

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero
Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

Har ila yau, dokar ta bai wa gwamna, idan har majalisar Sarakunan ta amince, ya iya tsigewa ko naÉ—a sabon Sarkin a duk masarautun.

Yanzu haka dai garin Kano yayi jim a daidai lokacin da majalisar ke shirin yin zama na musamman domin amincewa da gyaran.

Daily Trust ta rawaito cewa; wani babban jami’i a majalisar dokokin ya jaddada cewa babu wani da zai iya dakatar da yin gyaran domin sun ƙuduri niyyar yin shi tuntuni, wanda hakan ke nuni da cewa an daɗe ana shirin yin garambawul ga tsarin masarautun.

Sai dai shugaban marasa rinjaye Abdul Labaran Madari, ya tabbatar da cewa duk da cewa ƴaƴan jam’iyyar APC ba sa adawa da gyaran da aka yi niyyar aiwatarwa, amma sun dage cewa ba za a rusa ko ɗaya daga cikin masarautu biyar ɗin ba, kuma Sarkin (birnin) Kano na yanzu, Aminu Ado Bayero shi zai ci gaba da zama a kan kujerarsa.

Rahotanni sun bayyana cewa Sarkin Kano da Sarkin Bichi duk ba sa gari, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce kan illar rashin nasu.

Majiyoyi na nuni da cewa da zarar majalisar ta zartar da ƙudirin, nan take Gwamna Abba Kabir Yusuf zai sanya mata hannu, wanda hakan wataƙila zai iya maido da Sarki Sanusi II.

Sarki Muhammadu Sunusi II
Sarki Muhammadu Sunusi II

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Kabir YusufAminu AdokanoMasarautun KanoSanusi Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Halarci Bikin Rantsar Da Mahamat Deby A Chadi

Next Post

Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

6 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

22 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

LABARAI MASU NASABA

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Kano

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.