• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kallo Ya Koma Kano: Gwamna Abba Na Shirin Rattaba Hannu Kan Sabuwar Dokar Masarautar Kano

by Abubakar Sulaiman
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Kallo Ya Koma Kano: Gwamna Abba Na Shirin Rattaba Hannu Kan Sabuwar Dokar Masarautar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Abba Kabir Yusuf, na shirin rattaba hannu kan dokar majalisar masarautu da aka yi wa kwaskwarima yayin da majalisar dokokin Jihar Kano ke ci gaba da zama a yau domin kammala dokar.

Tun a jiya ne dai jami’an tsaro suka warwatsu a duk muhimman wurare na zauren majalisar lokacin da ƙudirin dokar da ke da nufin soke kafa masarautu biyar ya tsallake karatu na farko.

  • Sanata Barau Jibrin Ya Ƙaddamar Da Motocin Zirga-Zirga A Kano
  • Majalisar Dokokin Kano Za Ta Yi Wa Dokar Da Ta Tsige Sarki Sanusi II Kwaskwarima

Shugaban masu rinjaye Lawan Hussaini Chediyar Yan Gurasa ne, ya fara miƙa buƙatar yi wa dokar masarautun Kano (gyara mai lamba 2) ta 2024, manyan sauyin da ake niyyar yi zai jirkita tsarin masarautun da tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi a shekarar 2019.

Tsohuwar dokar ta 2019 wacce ta samar da sabbin masarautun Bichi da Rano da Gaya da Ƙaraye tare da (birnin) Kano, an yi gyare-gyare da dama a cikinta, inda aka yi  kwaskwarima a baya-bayan nan a shekarar 2020 da kuma 2023.

Sashe na 3(1) na dokar ya zayyana ikon waɗannan masarautun, inda kowannensu ke da ƙananan hukumomi da dama a ƙarƙashinsu.

Labarai Masu Nasaba

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Garan da aka yi a shekarar 2020 biyo bayan sauke Sarki Muhammadu Sanusi II, inda aka sake fasalin majalisar ta zama Sarkin Kano a matsayin mai jan ragamar na dindindin ga ragowar masarautun.

Sarkin Kano Aminu Ado Bayero
Sarkin Kano Aminu Ado Bayero

Har ila yau, dokar ta bai wa gwamna, idan har majalisar Sarakunan ta amince, ya iya tsigewa ko naÉ—a sabon Sarkin a duk masarautun.

Yanzu haka dai garin Kano yayi jim a daidai lokacin da majalisar ke shirin yin zama na musamman domin amincewa da gyaran.

Daily Trust ta rawaito cewa; wani babban jami’i a majalisar dokokin ya jaddada cewa babu wani da zai iya dakatar da yin gyaran domin sun ƙuduri niyyar yin shi tuntuni, wanda hakan ke nuni da cewa an daɗe ana shirin yin garambawul ga tsarin masarautun.

Sai dai shugaban marasa rinjaye Abdul Labaran Madari, ya tabbatar da cewa duk da cewa ƴaƴan jam’iyyar APC ba sa adawa da gyaran da aka yi niyyar aiwatarwa, amma sun dage cewa ba za a rusa ko ɗaya daga cikin masarautu biyar ɗin ba, kuma Sarkin (birnin) Kano na yanzu, Aminu Ado Bayero shi zai ci gaba da zama a kan kujerarsa.

Rahotanni sun bayyana cewa Sarkin Kano da Sarkin Bichi duk ba sa gari, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce kan illar rashin nasu.

Majiyoyi na nuni da cewa da zarar majalisar ta zartar da ƙudirin, nan take Gwamna Abba Kabir Yusuf zai sanya mata hannu, wanda hakan wataƙila zai iya maido da Sarki Sanusi II.

Sarki Muhammadu Sunusi II
Sarki Muhammadu Sunusi II

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abba Kabir YusufAminu AdokanoMasarautun KanoSanusi Lamido
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Halarci Bikin Rantsar Da Mahamat Deby A Chadi

Next Post

Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

7 minutes ago
Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

5 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

16 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

18 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

23 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

24 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro

LABARAI MASU NASABA

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

June 28, 2025
Za a Binne ÆŠantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne ÆŠantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren ÆŠan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.