ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Dokokin Kano Za Ta Yi Wa Dokar Da Ta Tsige Sarki Sanusi II Kwaskwarima

by Sadiq
2 years ago
Kano

Majalisar dokokin Jihar Kano ta kuduri aniyar yi wa dokar da ta tsige Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II gyara.

Tun da farko tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ne, ya yi amfani da dokar wajen tsige Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, Sarkin Kano na 14 a 2020.

  • Jirgin Sama Ya Yi Hatsari A Sama, Mutum 1 Ya Mutu 30 Sun Jikkata
  • Ƴansanda Sun Dakile Hari, Sun Ceto Mutane A Abuja

Shugaban masu rinjaye kuma wakilin mazabar Dala, Hussien Dala ne, ya gabatar da kudirin gyara dokar a yayin zaman majalisar na ranar Talata.

ADVERTISEMENT

A shekarar 2020, kafin a tsige Sanusi II, Ganduje ya rattaba hannu kan wata doka mai cike da cece-kuce, wadda ta raba masarautar Kano zuwa masarautu biyar.

Matakin dai ya haifar da cece-kuce da rarrabuwar kawuna a tsakanin masu ruwa da tsaki da al’ummar jihar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Magoya bayan Kwankwasiyya, sun yi ta kiranye-kiranye kan a mayar da Sanusi II kan karagar mulki tare da rushe masarautun Bichi, Gaya, Rano, da kuma Karaye.

A gefe guda kuma akwai wasu ƙungiyoyi da ke adawa da rushe sabbin masarautun, inda suke kallon yunkurin a matsayin wata gaba ta yin ramuwar gayya.

Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran jam’iyyar NNPP, mai mulki a Jihar Kano, a baya ya taba yin tsokaci kan batun yi wa masarautun kwaskwarima bayan Abba Kabir Yusuf ya zama gwamnan jihar..

“Mun yi yakin neman zabe kuma an san mu a Nijeriya, musamman a Kano, abin da muka nuna wa jama’a shi ne da yardar Allah duk ayyukan alheri da muka fara a lokacin muna gwamnati, wannan gwamna (Abba Kabir Yusuf) da tawagarsa za su dora daga inda muka tsaya,” in ji Kwankwaso.

“A matsayinmu na dattawan wannan tafiyar, za mu ci gaba da ba su shawarar su yi abin da ya dace, mun yi kokari ba za ce komai game da batun tsige Sarki, amma yanzu dama ta samu.

“Wadanda Allah Ya yi suka zama shugabanni a yanzu, su ne ke da alhakin yanke hukunci game da masarautun, za su sake duba lamarin su yi abin da ya dace,” in ji shi.

“Baya ga batun sauya Sarki, an raba masarautar zuwa gida biyar. Dukkaninsu za a sake duba su. Idan shugaba ya karbi mulki ko a matakin kasa, jiha ko karamar hukuma ne, yana gadar matsalolin da wasu zai iya sauya su, wasu kuma za su zama masu wahalar sauyawa.

“Muna da yakinin Allah zai bai wa gwamna (Abba Kabir Yusuf) hikimar warware matsalolin da aka kirkirar wa Jihar Kano domin kowa ya zauna lafiya a Jihar Kano,” in ji Kwankwaso.

Ana sa ran nan kwanaki masu zuwa majalisar dokokin Jihar Kano za ta ci gaba da yi wa dokar kwaskwarima.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Xi Ya Taya Zababben Shugaban Chadi Mahamat Deby Murna

Xi Ya Taya Zababben Shugaban Chadi Mahamat Deby Murna

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.