Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

An Kalubalanci Manoman Nasarawa Game Da Ilimin Kwamfuta

by Tayo Adelaja
September 17, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abdullahi, Lafia

An kalubalanci manoman Jihar Nasarawa da su rungumi ilimin na’urar kwamfuta domin bunkasa harkokin noma a jihar.

samndaads

Daraktan ma’aikata na karamar hukumar Lafia, Osabo Mohammed Ahmed ne ya yi wannan kalubalen a lokacin da yake bude taron horaswa na yini uku ga manoma wanda ya gudana a sakatariyar karamar hukumar Lafia.

Mohammed ya bayyana cewa duniya ta koma tamkar kauye guda, don haka akwai bukatar manoma su rungumi tsarin gudanar daharkokinsu a zamanance.

Da yake tabbattar da goyon bayan karamar hukumarsa ga shirin horaswar, Ahmed ya bayyana cewa noma mabudi ne na cigaba ga kowace al’umma.

Tun farko, babban manajan kamfanin kasuwancin kayan gona Steben Maduokor, ya ce dalilin bada horon shi ne don ilmantar da manoma kan harkar kasuwanci ta dandalin intanet.

Daga nan, ya yaba wa babbar bankin kasa da bankin manoma, ma’aikatar gona ta tarraya da sauran masu ruwa da tsaki kan mara wa hakar noma baya.

Maduokor ya bayyana cewa shirin horaswar zai taima wa manoma da ilimin inganta shuki da girbi.

Da yake tofa albarkacin bakinsa yayin taron, wakilin babban banki kasa, Ogidi Akim ya sanar cewa babban banki kasa na da shirye-shirye masu yawa don amfanin manoma. Sannan ya gargadi jama’a kan bada cin-hanci ga wani kafin kai ga samun tallafin kudi daga babban bankin, tare da jaddada cewa bankin ba ya karbar ko sisin kwabo kafin tallafa wa shiri.

Wasu daga cikin mahalarta taron da suka zanta da manema labarai, sun nuna godiyarsu ga wadanda suka shirya taron, tare da bada tabbacin cewa za su yi amfani da irin darussan da suka koya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Siyasar Kano: An Gano Dalilin Rikicin Sanata Gaya Da Kawu Sumaila

Next Post

Sarkin Kano: Idan Har Bai Ji Tsoron Shekau Ba, Me Ya Sa Zai Ji Tsoron Buhari?

RelatedPosts

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

by Daurawa Daurawa
18 hours ago
0

Mai taimakawa gwamna Masari akan wayar da kan jama’a akan...

’Yan Sandan Kano Sun Cafke Mace Mai Garkuwa Da Mutane

’Yan Sandan Kano Sun Cafke Mace Mai Garkuwa Da Mutane

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta shaida cewar wata mace...

Ta’aziyar Rasuwar Sam Nda Isaiah

Sam Nda-Isaiah Ya Rasu Lokacin Da Ake Tsananin Bukatar Gudunmawarsa – Jami’ar Jos

by Sulaiman Ibrahim
5 days ago
0

Shugabannin jami’ar Jos sun bayyana rashin jin dadinsu dangane da...

Next Post

Sarkin Kano: Idan Har Bai Ji Tsoron Shekau Ba, Me Ya Sa Zai Ji Tsoron Buhari?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version