• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Da Ke Gaban Finidi George

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Finidi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan da hukumar kallon kafar Nijeriya, NFF ta nada Finidi George a matakin sabon kociyan Super Eagles, tuni masana suka fara sharhi a kan irin kalubalen da ke gaban tsohon dan wasan na Nijeriya.

Kafin a nada shi a matsayin koci na dindindin Finidi George ya yi watanni 20 yana aikin mataimakin Jose Santos Peseiro, wanda ya ajiye aikin, bayan kammala gasar cin kofin nahiyar Afirka da Super Eagles ta yi ta biyu a Ivory Coast a bana.

  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida Ta Nada Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnatin Kaduna Uban Kungiya
  • Shawara Daga Likita Kan Tiyatar Kara Girman Nono Da Mazaunai

Haka kuma ya ja ragamar tawagar Nijeriya a matakin kociyan rikon kwarya a wasan sa-da zumunta biyu da ta buga a Morocco a watan jiya sannan ya kuma doke Ghana 2-1 a wasan farko, hakan ya kawo karshen rashin nasara a kan Ghana daga Super Eagles cikin shekara 18, amma an doke shi 2-0 a karawa da Mali a wasan na sada zumunta.

George, wanda yana cikin ‘yan wasan da suka dauki kofin nahiyar Afirka a Super Eagles a 1994 a Tunisia, ya buga mata wasanni 62, ya wakilce ta a gasar kofin duniya a 1994 da 1998.

Haka kuma ya lashe lambar zinare da ta azurfa da ta tagulla a gasar kofin nahiyar Afirka a 1992 da 1994 da 2000 da kuma 2002, sannan Finidi mai shekara 52 tsohon dan kwal-lon Ajad da Real Betis ya fara buga wasa a Calabar Robers da Sharks FC daga nan ya je nahiyar Turai ya buga wasa a kungiyoyin Ajad da Real Betis.

Labarai Masu Nasaba

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

Shi ne ya bai wa Rashidi Yakini, kwallon da Nijeriya ta fara ci a gasar kofin duniya a karawa da Bulgaria a Amurka ranar 19 ga watan Yunin 1994, sannan aikin da aka bai wa George shi ne ya yi kokarin ganin ya kai Super Eagles gasar cin kofin duniya da za a yi a 2026 a Amurka da Canada da kuma Mexico.

Kenan ya zama wajibi Nijeriya ta doke Afirka ta Kudu a Uyo da kuma Jamhuriyar Benin a Abidjan a wasannin neman shiga gasar kofin duniya da suke gabanta saboda kawo yanzu Super Eagles tana ta uku a rukuni na uku a neman gurbin shiga gasar kofin duni-ya, biye da Rwanda da kuma Afirka ta Kudu.

Banda gasar cin kofin duniya da ake fatan Finidi zai iya jagorantar Nijeriya, akwai buka-tar hada kan ‘yan wasan kasar domin gina sabuwar tawagar da za ta dade ana damawa da ita a fagen kwallon kafa.

Sannan akwai nada sabon kyaftin, bayan da ake ganin abu ne mai wahala dan wasa Ahamd Musa ya ci gaba da zama kyaftin din tawagar ta Super Eagles, nan ma wasu suna ganin dan wasan baya kuma mataimakin Ahmad din, William Trost-Ekong, wanda kusan shi ne ya jagoranci tawagar har aka kammala wasannin Afirka da Nijeriya ta je wasan karshe shi ne ya kamata ya zama jagoran Super Eagles din.

Wani abu da ake fatan Finidi zai yi shi ne bawa matasa dama domin suma su samu damar bayyana kansu a matsayin ‘yan wasan Super Eagles domin Nijeriya akwai matasan ‘yan wasa da kawai dama suke bukata domin nuna kansu a duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Finidi GeorgeNFFSuper eagle
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyawawan ‘Yan Mata Da Suke Shiga Harkar Fim Suna Bata Rayuwarsu -Kyauta Dillaliya

Next Post

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron OIC Karo Na 15 

Related

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
Wasanni

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

2 hours ago
Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa
Wasanni

Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa

3 days ago
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu
Wasanni

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Wasan Ƙarshe Bayan Doke Afrika Ta Kudu

4 days ago
Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo
Wasanni

Oshoala Za Ta Yi Ritaya Daga Buga Wa Nijeriya Ƙwallo

4 days ago
Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro
Wasanni

Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro

5 days ago
Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa
Wasanni

Kamfanin Puma Zai Biya Man City Fam Biliyan 1 A Shekara 10 Domin Samar Wa Kungiyar Kayan Wasa

7 days ago
Next Post
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron OIC Karo Na 15 

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron OIC Karo Na 15 

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.