• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Da Ke Gaban Finidi George

byAbba Ibrahim Wada
1 year ago
Finidi

Bayan da hukumar kallon kafar Nijeriya, NFF ta nada Finidi George a matakin sabon kociyan Super Eagles, tuni masana suka fara sharhi a kan irin kalubalen da ke gaban tsohon dan wasan na Nijeriya.

Kafin a nada shi a matsayin koci na dindindin Finidi George ya yi watanni 20 yana aikin mataimakin Jose Santos Peseiro, wanda ya ajiye aikin, bayan kammala gasar cin kofin nahiyar Afirka da Super Eagles ta yi ta biyu a Ivory Coast a bana.

  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida Ta Nada Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnatin Kaduna Uban Kungiya
  • Shawara Daga Likita Kan Tiyatar Kara Girman Nono Da Mazaunai

Haka kuma ya ja ragamar tawagar Nijeriya a matakin kociyan rikon kwarya a wasan sa-da zumunta biyu da ta buga a Morocco a watan jiya sannan ya kuma doke Ghana 2-1 a wasan farko, hakan ya kawo karshen rashin nasara a kan Ghana daga Super Eagles cikin shekara 18, amma an doke shi 2-0 a karawa da Mali a wasan na sada zumunta.

George, wanda yana cikin ‘yan wasan da suka dauki kofin nahiyar Afirka a Super Eagles a 1994 a Tunisia, ya buga mata wasanni 62, ya wakilce ta a gasar kofin duniya a 1994 da 1998.

Haka kuma ya lashe lambar zinare da ta azurfa da ta tagulla a gasar kofin nahiyar Afirka a 1992 da 1994 da 2000 da kuma 2002, sannan Finidi mai shekara 52 tsohon dan kwal-lon Ajad da Real Betis ya fara buga wasa a Calabar Robers da Sharks FC daga nan ya je nahiyar Turai ya buga wasa a kungiyoyin Ajad da Real Betis.

LABARAI MASU NASABA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Shi ne ya bai wa Rashidi Yakini, kwallon da Nijeriya ta fara ci a gasar kofin duniya a karawa da Bulgaria a Amurka ranar 19 ga watan Yunin 1994, sannan aikin da aka bai wa George shi ne ya yi kokarin ganin ya kai Super Eagles gasar cin kofin duniya da za a yi a 2026 a Amurka da Canada da kuma Mexico.

Kenan ya zama wajibi Nijeriya ta doke Afirka ta Kudu a Uyo da kuma Jamhuriyar Benin a Abidjan a wasannin neman shiga gasar kofin duniya da suke gabanta saboda kawo yanzu Super Eagles tana ta uku a rukuni na uku a neman gurbin shiga gasar kofin duni-ya, biye da Rwanda da kuma Afirka ta Kudu.

Banda gasar cin kofin duniya da ake fatan Finidi zai iya jagorantar Nijeriya, akwai buka-tar hada kan ‘yan wasan kasar domin gina sabuwar tawagar da za ta dade ana damawa da ita a fagen kwallon kafa.

Sannan akwai nada sabon kyaftin, bayan da ake ganin abu ne mai wahala dan wasa Ahamd Musa ya ci gaba da zama kyaftin din tawagar ta Super Eagles, nan ma wasu suna ganin dan wasan baya kuma mataimakin Ahmad din, William Trost-Ekong, wanda kusan shi ne ya jagoranci tawagar har aka kammala wasannin Afirka da Nijeriya ta je wasan karshe shi ne ya kamata ya zama jagoran Super Eagles din.

Wani abu da ake fatan Finidi zai yi shi ne bawa matasa dama domin suma su samu damar bayyana kansu a matsayin ‘yan wasan Super Eagles domin Nijeriya akwai matasan ‘yan wasa da kawai dama suke bukata domin nuna kansu a duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron OIC Karo Na 15 

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron OIC Karo Na 15 

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version