ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kalubalen Da Ke Gaban Finidi George

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
Finidi

Bayan da hukumar kallon kafar Nijeriya, NFF ta nada Finidi George a matakin sabon kociyan Super Eagles, tuni masana suka fara sharhi a kan irin kalubalen da ke gaban tsohon dan wasan na Nijeriya.

Kafin a nada shi a matsayin koci na dindindin Finidi George ya yi watanni 20 yana aikin mataimakin Jose Santos Peseiro, wanda ya ajiye aikin, bayan kammala gasar cin kofin nahiyar Afirka da Super Eagles ta yi ta biyu a Ivory Coast a bana.

  • Ƙungiyar ‘Yan Jarida Ta Nada Shugaban Ma’aikatan Fadar Gwamnatin Kaduna Uban Kungiya
  • Shawara Daga Likita Kan Tiyatar Kara Girman Nono Da Mazaunai

Haka kuma ya ja ragamar tawagar Nijeriya a matakin kociyan rikon kwarya a wasan sa-da zumunta biyu da ta buga a Morocco a watan jiya sannan ya kuma doke Ghana 2-1 a wasan farko, hakan ya kawo karshen rashin nasara a kan Ghana daga Super Eagles cikin shekara 18, amma an doke shi 2-0 a karawa da Mali a wasan na sada zumunta.

ADVERTISEMENT

George, wanda yana cikin ‘yan wasan da suka dauki kofin nahiyar Afirka a Super Eagles a 1994 a Tunisia, ya buga mata wasanni 62, ya wakilce ta a gasar kofin duniya a 1994 da 1998.

Haka kuma ya lashe lambar zinare da ta azurfa da ta tagulla a gasar kofin nahiyar Afirka a 1992 da 1994 da 2000 da kuma 2002, sannan Finidi mai shekara 52 tsohon dan kwal-lon Ajad da Real Betis ya fara buga wasa a Calabar Robers da Sharks FC daga nan ya je nahiyar Turai ya buga wasa a kungiyoyin Ajad da Real Betis.

LABARAI MASU NASABA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

Shi ne ya bai wa Rashidi Yakini, kwallon da Nijeriya ta fara ci a gasar kofin duniya a karawa da Bulgaria a Amurka ranar 19 ga watan Yunin 1994, sannan aikin da aka bai wa George shi ne ya yi kokarin ganin ya kai Super Eagles gasar cin kofin duniya da za a yi a 2026 a Amurka da Canada da kuma Mexico.

Kenan ya zama wajibi Nijeriya ta doke Afirka ta Kudu a Uyo da kuma Jamhuriyar Benin a Abidjan a wasannin neman shiga gasar kofin duniya da suke gabanta saboda kawo yanzu Super Eagles tana ta uku a rukuni na uku a neman gurbin shiga gasar kofin duni-ya, biye da Rwanda da kuma Afirka ta Kudu.

Banda gasar cin kofin duniya da ake fatan Finidi zai iya jagorantar Nijeriya, akwai buka-tar hada kan ‘yan wasan kasar domin gina sabuwar tawagar da za ta dade ana damawa da ita a fagen kwallon kafa.

Sannan akwai nada sabon kyaftin, bayan da ake ganin abu ne mai wahala dan wasa Ahamd Musa ya ci gaba da zama kyaftin din tawagar ta Super Eagles, nan ma wasu suna ganin dan wasan baya kuma mataimakin Ahmad din, William Trost-Ekong, wanda kusan shi ne ya jagoranci tawagar har aka kammala wasannin Afirka da Nijeriya ta je wasan karshe shi ne ya kamata ya zama jagoran Super Eagles din.

Wani abu da ake fatan Finidi zai yi shi ne bawa matasa dama domin suma su samu damar bayyana kansu a matsayin ‘yan wasan Super Eagles domin Nijeriya akwai matasan ‘yan wasa da kawai dama suke bukata domin nuna kansu a duniya.

Finidi
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta
Adabi

Super Eagles Ta Tafi Poland Domin Wasan Sada Zumunta

May 31, 2026
Next Post
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron OIC Karo Na 15 

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron OIC Karo Na 15 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.