• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kangin Dalar Amurka: Yadda Nijeriya Za Ta Dauki Darasi Daga Kasashen Duniya

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Kangin Dalar Amurka: Yadda Nijeriya Za Ta Dauki Darasi Daga Kasashen Duniya

A woman sells crayfish at a Mile 12 Market in Lagos, Nigeria, Friday, Feb. 16, 2024. Nigerians are facing one of the West African nation's worst economic crises in as many years triggered by a surging inflation rate which follows monetary policies that have dipped the local currency to an all-time low against the dollar, provoking anger and protests across the country. (AP Photo/Mansur Ibrahim)

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kimanin wata bakwai da suka gabata, na rubuta sharhi mai taken “Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka”. Na kawo misalai da kasashe irin su Argentina, Brazil da Bolivia da suka fara amfani da kudin kasar Sin, Renminbi a kasuwancin dake tsakaninsu da Sin da kuma yadda lamarin yake kara samun karbuwa a yankin Latin Amurka da Caribbean.

A wancan lokacin, na yi hasashen Dala 1 na iya zarta Naira 1,000, kuma tabbas hasashe nawa ya zama gaskiya, domin yanzu haka farashin gwamnati na kwan-gaba-kwan-baya ne a tsakanin 1,500 kowace dala.
A sakamakon haka, ‘yan Nijeriya na fuskantar daya daga cikin mafi munin tabarbarewar tattalin arziki da ba a ga irinsa ba cikin shekaru da dama sakamakon hauhawar farashin kayayyaki sanadiyyar kangin Dalar Amurka.

  • Mazauna Yankunan Karkarar Sin Sun Samu Karin Kyautatuwar Rayuwa

Alkaluman gwamnati na baya-bayan nan da aka fitar, sun nuna hauhawar farashin kayayyaki a watan Janairu ya karu zuwa kashi 29.9%, mafi girma tun daga shekarar 1996. Darajar kudinmu ta karye da kashi 230% a kasa da shekara guda kacal!
Wannan abu ya tsaya mana a kahon zuci. Ya kamata a hanzarta lalubo bakin zaren magance lamarin. Tun da tattalin arzikinmu galibi ya fi dogara ne kan shigo da kaya daga kasashen waje, ya dace a mayar da hankali wajen habaka kasuwanci da kasashen da za mu iya hulda da su ba tare da Dalar Amurka ba.

Wannan lokaci zai zama mafi dacewa na farfado da yarjejeniyar musanyar kudi a tsakanin Nijeriya da Sin wanda aka so yi a shekarar 2018, ta kimanin Naira Biliyan 720 kwatankwacin RMB Biliyan 15 (a wancan lokaci), amma wasu suka yi wa abin kafar ungulu.

Tabbas idan aka yi haka, zai rage mana radadin kangin dala, domin zuwa watan Nuwambar 2023, kasuwancin dake tsakanin Sin da Nijeriya ya kai na Dala Biliyan 22.6 (sama da Naira Tiriliyan 35). Kuma ana sa ran wannan ya karu saboda yadda kasar Sin ta fi kowacce huldar kasuwanci da kasashen waje a duniya, sannan Najeriya ita ce ta uku a yawan kasuwancin da Sin ke yi da Afirka.
Kamar yadda Karamar Jakadiyar kasar Sin a Nijeriya Yan Yuqing, ta bayyana a kwanan baya, “A shekarun baya-bayan nan, hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Nijeriya a fannonin filin jirgin sama, tashar jiragen ruwa, layin dogo, hanyoyin mota, hanyoyin sadarwa da sauran ababen more rayuwa sun samu babbar nasara. ” Ta bayyana hakan ne a Legas a wajen bikin lale marhabin da isowar jirgin ruwa na CMA CGM Scandola, wanda ya kasance mafi girman dakon kwantena da ya ziyarci tashar ruwan Nijeriya a bana zuwa yanzu.

Labarai Masu Nasaba

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Sabo da siyasar duniya, Amurka za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin ta ci gaba da tilasta wa Nijeriya amfani da Dalarta a kasuwancin kasashen waje, amma kuma mai daki shi ya san wurin da yake masa yoyo, kangin da Dalar ta jefa mu ya yi yawa, me ya sa za mu ci gaba da kashe kanmu don kawai wata kasa ta ci gaba da jan zarenta a duniya?

A wani littafinsa na baya-bayan nan, “Edible Economics: A Hungry Economist Explains the World”, masanin tattalin arziki dan asalin Koriya ta Kudu na Jami’ar London, Ha-Joon Chang, ya yi tsokacin cewa, “Duk da kasashen Afirka sun sha wahala fiye da yadda kasashen Latin Amurka suka sha daga manufofin yarjejeniyar Washington (wacce John Williamson ya gabatar a 1989), amma kuma sun gaza fitowa baro-baro a fili su yi watsi da su (manufofin), ganin yadda suka fi dogaro da cibiyoyin Washington don samun kudade. Amma kuma, a cikin shekaru goma da suka wuce, ana samun karuwar amincewa da bukatar lallai kasa ta yi wa kanta kiyamullaili fiye da abin da Yarjejeniyar Washington ta ba da shawara a kai.”

Akwai kasashe da suka samar wa kansu mafita, misali, Rasha da Sin suna cinikayya ta amfani da kudinsu Yuan da Rubles maimakon Dalar Amurka. Haka nan masu sayen man Rasha a Indiya suna biyan galibin kudin ne da ko dai kudin Rashar ko kuma Dirham na Hadaddiyar Daular Larabawa. Ko a nan Afirka ma, Kenya ta kulla yarjejeniya da Kamfanin Mai na Saudiyya (Aramco) da na Abu Dhabi (Adnoc) da za su rika shigo mata da fetur da gas, ita kuma tana biya da kudin kasarta na Shillings. Don haka, ya kamata Nijeriya ta bi sawu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ChinaDalar AmurkaDollarKasashen duniyaNijeriyaRashaSinTattalin ArzikiUS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Sokoto Ta Buƙaci Gwamnati Da Ta Faɗaɗa Shirin Ciyar Da Abinci A Watan Ramadan

Next Post

Sin Ta Kira Taron Tattauna Kan Rahoton Gwamnati

Related

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka
Ra'ayi Riga

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

21 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

4 days ago
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
Ra'ayi Riga

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

6 days ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

7 days ago
Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
Ra'ayi Riga

Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba

1 week ago
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ra'ayi Riga

Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya

2 weeks ago
Next Post
Sin Ta Kira Taron Tattauna Kan Rahoton Gwamnati

Sin Ta Kira Taron Tattauna Kan Rahoton Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.