ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 22, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kangin Dalar Amurka: Yadda Nijeriya Za Ta Dauki Darasi Daga Kasashen Duniya

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
A woman sells crayfish at a Mile 12 Market in Lagos, Nigeria, Friday, Feb. 16, 2024. Nigerians are facing one of the West African nation's worst economic crises in as many years triggered by a surging inflation rate which follows monetary policies that have dipped the local currency to an all-time low against the dollar, provoking anger and protests across the country. (AP Photo/Mansur Ibrahim)

A woman sells crayfish at a Mile 12 Market in Lagos, Nigeria, Friday, Feb. 16, 2024. Nigerians are facing one of the West African nation's worst economic crises in as many years triggered by a surging inflation rate which follows monetary policies that have dipped the local currency to an all-time low against the dollar, provoking anger and protests across the country. (AP Photo/Mansur Ibrahim)

Kimanin wata bakwai da suka gabata, na rubuta sharhi mai taken “Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka”. Na kawo misalai da kasashe irin su Argentina, Brazil da Bolivia da suka fara amfani da kudin kasar Sin, Renminbi a kasuwancin dake tsakaninsu da Sin da kuma yadda lamarin yake kara samun karbuwa a yankin Latin Amurka da Caribbean.

A wancan lokacin, na yi hasashen Dala 1 na iya zarta Naira 1,000, kuma tabbas hasashe nawa ya zama gaskiya, domin yanzu haka farashin gwamnati na kwan-gaba-kwan-baya ne a tsakanin 1,500 kowace dala.
A sakamakon haka, ‘yan Nijeriya na fuskantar daya daga cikin mafi munin tabarbarewar tattalin arziki da ba a ga irinsa ba cikin shekaru da dama sakamakon hauhawar farashin kayayyaki sanadiyyar kangin Dalar Amurka.

  • Mazauna Yankunan Karkarar Sin Sun Samu Karin Kyautatuwar Rayuwa

Alkaluman gwamnati na baya-bayan nan da aka fitar, sun nuna hauhawar farashin kayayyaki a watan Janairu ya karu zuwa kashi 29.9%, mafi girma tun daga shekarar 1996. Darajar kudinmu ta karye da kashi 230% a kasa da shekara guda kacal!
Wannan abu ya tsaya mana a kahon zuci. Ya kamata a hanzarta lalubo bakin zaren magance lamarin. Tun da tattalin arzikinmu galibi ya fi dogara ne kan shigo da kaya daga kasashen waje, ya dace a mayar da hankali wajen habaka kasuwanci da kasashen da za mu iya hulda da su ba tare da Dalar Amurka ba.

ADVERTISEMENT

Wannan lokaci zai zama mafi dacewa na farfado da yarjejeniyar musanyar kudi a tsakanin Nijeriya da Sin wanda aka so yi a shekarar 2018, ta kimanin Naira Biliyan 720 kwatankwacin RMB Biliyan 15 (a wancan lokaci), amma wasu suka yi wa abin kafar ungulu.

Tabbas idan aka yi haka, zai rage mana radadin kangin dala, domin zuwa watan Nuwambar 2023, kasuwancin dake tsakanin Sin da Nijeriya ya kai na Dala Biliyan 22.6 (sama da Naira Tiriliyan 35). Kuma ana sa ran wannan ya karu saboda yadda kasar Sin ta fi kowacce huldar kasuwanci da kasashen waje a duniya, sannan Najeriya ita ce ta uku a yawan kasuwancin da Sin ke yi da Afirka.
Kamar yadda Karamar Jakadiyar kasar Sin a Nijeriya Yan Yuqing, ta bayyana a kwanan baya, “A shekarun baya-bayan nan, hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Nijeriya a fannonin filin jirgin sama, tashar jiragen ruwa, layin dogo, hanyoyin mota, hanyoyin sadarwa da sauran ababen more rayuwa sun samu babbar nasara. ” Ta bayyana hakan ne a Legas a wajen bikin lale marhabin da isowar jirgin ruwa na CMA CGM Scandola, wanda ya kasance mafi girman dakon kwantena da ya ziyarci tashar ruwan Nijeriya a bana zuwa yanzu.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

Sabo da siyasar duniya, Amurka za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin ta ci gaba da tilasta wa Nijeriya amfani da Dalarta a kasuwancin kasashen waje, amma kuma mai daki shi ya san wurin da yake masa yoyo, kangin da Dalar ta jefa mu ya yi yawa, me ya sa za mu ci gaba da kashe kanmu don kawai wata kasa ta ci gaba da jan zarenta a duniya?

A wani littafinsa na baya-bayan nan, “Edible Economics: A Hungry Economist Explains the World”, masanin tattalin arziki dan asalin Koriya ta Kudu na Jami’ar London, Ha-Joon Chang, ya yi tsokacin cewa, “Duk da kasashen Afirka sun sha wahala fiye da yadda kasashen Latin Amurka suka sha daga manufofin yarjejeniyar Washington (wacce John Williamson ya gabatar a 1989), amma kuma sun gaza fitowa baro-baro a fili su yi watsi da su (manufofin), ganin yadda suka fi dogaro da cibiyoyin Washington don samun kudade. Amma kuma, a cikin shekaru goma da suka wuce, ana samun karuwar amincewa da bukatar lallai kasa ta yi wa kanta kiyamullaili fiye da abin da Yarjejeniyar Washington ta ba da shawara a kai.”

Akwai kasashe da suka samar wa kansu mafita, misali, Rasha da Sin suna cinikayya ta amfani da kudinsu Yuan da Rubles maimakon Dalar Amurka. Haka nan masu sayen man Rasha a Indiya suna biyan galibin kudin ne da ko dai kudin Rashar ko kuma Dirham na Hadaddiyar Daular Larabawa. Ko a nan Afirka ma, Kenya ta kulla yarjejeniya da Kamfanin Mai na Saudiyya (Aramco) da na Abu Dhabi (Adnoc) da za su rika shigo mata da fetur da gas, ita kuma tana biya da kudin kasarta na Shillings. Don haka, ya kamata Nijeriya ta bi sawu.

dala
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya
Ra'ayi Riga

Sin Na Daukar hakikanan Matakan Gina Kyakkaywar Makomar Al’ummun Sin Da Afirka Ta Bai Daya

June 19, 2026
A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”
Ra'ayi Riga

A Yi Watsi Da Wannan “Mummunan Teburi”

June 18, 2026
Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata
Ra'ayi Riga

Daga Taklamakan Zuwa Sahara: Yadda Hamada Ke “Haifar” Da Fata

June 17, 2026
Next Post
Sin Ta Kira Taron Tattauna Kan Rahoton Gwamnati

Sin Ta Kira Taron Tattauna Kan Rahoton Gwamnati

LABARAI MASU NASABA

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Mataimakin Sakataren Majalisar Koli Ta Tsaron Iran 

Ministan Wajen Sin Ya Gana Da Mataimakin Sakataren Majalisar Koli Ta Tsaron Iran 

June 22, 2026
Hada-hadar Sayayya Ta Gudana Bisa Daidaito Yayin Bikin Gargajiya Na Dragon Boat Na Bana

Hada-hadar Sayayya Ta Gudana Bisa Daidaito Yayin Bikin Gargajiya Na Dragon Boat Na Bana

June 22, 2026
Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti

Ya Kamata Farashin Siminti Ya Sauka — Umahi Ga Masana’antun Siminti

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi Masu Ɓoye Gas Ɗin Girki

June 22, 2026
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Tsare Sowore A Gidan Yarin Kuje

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

Yanzu-Yanzu: An Kashe Manoma 18 Da Raunata Wasu A Wani Sabon Hari A Filato

June 22, 2026
Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

Yanzu-Yanzu: Firaiministan Birtaniya Keir Starmer Ya Yi Murabus

June 22, 2026
Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Sace, Sun Daƙile Hari A Kaduna Da Zamfara

June 22, 2026
Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

Fisatattun Matasa Sun Ƙone Wata Mata Ƙurmus Kan Jita-Jitar Satar Yara A Kaduna

June 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.