• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na More Ci Gabanta Da Kasashen Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Na More Ci Gabanta Da Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Da an fara daga safe har yamma, mutane suna zuwa suna kallon kaya suna tambaya, suna karbar adireshi, to ka ga duk kuwa Alhamdulillah, kwalliya ta biya kudin sabulu a kan wannan ziyarar.” Yadda Mista Saidu Mustapha, jami’i a kwamitin sa kaimin harkokin fitar da kayayyaki zuwa ketare ta Nijeriya(NEPC), ya bayyana a ziyararsa birnin Shanghai don halartar bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin(CIIE) ke nan. Ya ce, yana sa ran kara halartar bikin a shekara mai zuwa.

A ranar 10 ga wata, an kawo karshen bikin CIIE karo na shida a birnin Shanghai da ke gabashin kasar Sin.

  • Afirka CDC Ta Bude Dakin Gwaje-gwajen Bincike Da Sin Ta Samar
  • Bikin Baje Kolin CIIE: Kasashen Afirka Kar Ku Yarda A Bar Ku A Baya

A gun bikin na bana, ‘yan kasuwa daga Nijeriya sun baje kolin ridi da busashen citta da dawa da gyada da dai sauran amfanin gona da ma ma’adinai da ake samu a kasar. Ibrahim A. Ahmed, kwamishinan kula da harkokin cinikayya da zuba jari a karamin ofishin jakadancin Nijeriya da ke birnin Shanghai ya ce, akwai kayayyaki da dama da suke shiga sahun gaba a Afirka ta fannin yawansu da ingancinsu, kuma CIIE ya samar wa Nijeriya wani dandali na nuna su ga duniya. Ya ce, “Shekaru shida a jere ne kasar Sin ta shirya wannan kasaitaccen biki na CIIE, wanda ya shaida niyyarta ta kara bude kofarta da ma habaka shigowa da kayayyaki, kuma hakan ya samar da damammaki ga kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa na habaka cinikinsu da ma janyo jarin waje.”

Ban da kayayyaki na Nijeriya, dimbin kayayyakin Afirka da aka baje kolinsu a gun bikin na wannan shekara su ma sun yi matukar jawo hankalin masu halartar bikin.

Idi Moussa Mahamadou, dan kasuwa ne daga birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar, wanda ya halarci bikin CIIE a karo na farko. Yawancin kayayyakin da ya kawo a wannan karo, amfanin gona ne, dake kunshe da dawa, da gyada, da zobo, da waken soya, da ridi, da zogale da kwaron arabic da sauransu. Ya ce yana fatan tallata kayan Nijar ga kasar Sin da ma duk duniya, don bada taimakonsa ga ci gaban kasar.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

A cikin ’yan shekarun baya, kasar Sin ta yi ta sa kaimin shigowa da kayayyaki masu inganci na kasa da kasa, don duniya ta more babbar kasuwarta da ma ci gabanta. Tun daga shekarar 2018 kuma, kasar ta fara shirya bikin CIIE a farkon watan Nuwamban kowace shekara, wanda ya kasance irinsa na farko a duniya da ke mai da hankali musamman a kan kayayyakin da ake shigowa da su daga ketare.

A bana, akwai kasashe 11 da suka halarci bikin a karo na farko, kuma daga cikinsu guda 7 kasashen Afirka ne. Karin kasashen Afirka da kamfanoninsu suna zuwa don nuna kayayyakinsu ga kasashen duniya. A cewar Stephen Kargbo, wakilin kungiyar raya masana’antu ta Majalisar Dinkin Duniya(UNIDO) a kasar Sin, dimbin kamfanoni na kasarsa, wato Saliyo, da na sauran kasashe daban daban dake nahiyar Afirka, sun halarci bikin CIIE na bana, inda suka samu damar nuna fasahohi, da kayayyakinsu a wannan muhimmin dandali na kasa da kasa. Ya ce, “Bikin CIIE na kasar Sin ya ba mabambantan kasashe damar more ci gaban tattalin arzikinta, kana kasar ba za ta bar kowa a baya ba.” (Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaCGTNSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Bada Umarnin Sake Zabe A Wasu Sassan Jihar Kogi

Next Post

Majalisar Ɗinkin Duniya Da Tarayyar Turai Sun Miƙa Cibiyar Kula Da Matan Da Aka Ci Zarafinsu Ga Jihar Sokoto

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

1 day ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

1 day ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

1 day ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

1 day ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

1 day ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

2 days ago
Next Post
Majalisar Ɗinkin Duniya Da Tarayyar Turai Sun Miƙa Cibiyar Kula Da Matan Da Aka Ci Zarafinsu Ga Jihar Sokoto

Majalisar Ɗinkin Duniya Da Tarayyar Turai Sun Miƙa Cibiyar Kula Da Matan Da Aka Ci Zarafinsu Ga Jihar Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.