• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Na More Ci Gabanta Da Kasashen Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin Na More Ci Gabanta Da Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Da an fara daga safe har yamma, mutane suna zuwa suna kallon kaya suna tambaya, suna karbar adireshi, to ka ga duk kuwa Alhamdulillah, kwalliya ta biya kudin sabulu a kan wannan ziyarar.” Yadda Mista Saidu Mustapha, jami’i a kwamitin sa kaimin harkokin fitar da kayayyaki zuwa ketare ta Nijeriya(NEPC), ya bayyana a ziyararsa birnin Shanghai don halartar bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin(CIIE) ke nan. Ya ce, yana sa ran kara halartar bikin a shekara mai zuwa.

A ranar 10 ga wata, an kawo karshen bikin CIIE karo na shida a birnin Shanghai da ke gabashin kasar Sin.

  • Afirka CDC Ta Bude Dakin Gwaje-gwajen Bincike Da Sin Ta Samar
  • Bikin Baje Kolin CIIE: Kasashen Afirka Kar Ku Yarda A Bar Ku A Baya

A gun bikin na bana, ‘yan kasuwa daga Nijeriya sun baje kolin ridi da busashen citta da dawa da gyada da dai sauran amfanin gona da ma ma’adinai da ake samu a kasar. Ibrahim A. Ahmed, kwamishinan kula da harkokin cinikayya da zuba jari a karamin ofishin jakadancin Nijeriya da ke birnin Shanghai ya ce, akwai kayayyaki da dama da suke shiga sahun gaba a Afirka ta fannin yawansu da ingancinsu, kuma CIIE ya samar wa Nijeriya wani dandali na nuna su ga duniya. Ya ce, “Shekaru shida a jere ne kasar Sin ta shirya wannan kasaitaccen biki na CIIE, wanda ya shaida niyyarta ta kara bude kofarta da ma habaka shigowa da kayayyaki, kuma hakan ya samar da damammaki ga kasashen Afirka da ma sauran kasashe masu tasowa na habaka cinikinsu da ma janyo jarin waje.”

Ban da kayayyaki na Nijeriya, dimbin kayayyakin Afirka da aka baje kolinsu a gun bikin na wannan shekara su ma sun yi matukar jawo hankalin masu halartar bikin.

Idi Moussa Mahamadou, dan kasuwa ne daga birnin Yamai na Jamhuriyar Nijar, wanda ya halarci bikin CIIE a karo na farko. Yawancin kayayyakin da ya kawo a wannan karo, amfanin gona ne, dake kunshe da dawa, da gyada, da zobo, da waken soya, da ridi, da zogale da kwaron arabic da sauransu. Ya ce yana fatan tallata kayan Nijar ga kasar Sin da ma duk duniya, don bada taimakonsa ga ci gaban kasar.

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

A cikin ’yan shekarun baya, kasar Sin ta yi ta sa kaimin shigowa da kayayyaki masu inganci na kasa da kasa, don duniya ta more babbar kasuwarta da ma ci gabanta. Tun daga shekarar 2018 kuma, kasar ta fara shirya bikin CIIE a farkon watan Nuwamban kowace shekara, wanda ya kasance irinsa na farko a duniya da ke mai da hankali musamman a kan kayayyakin da ake shigowa da su daga ketare.

A bana, akwai kasashe 11 da suka halarci bikin a karo na farko, kuma daga cikinsu guda 7 kasashen Afirka ne. Karin kasashen Afirka da kamfanoninsu suna zuwa don nuna kayayyakinsu ga kasashen duniya. A cewar Stephen Kargbo, wakilin kungiyar raya masana’antu ta Majalisar Dinkin Duniya(UNIDO) a kasar Sin, dimbin kamfanoni na kasarsa, wato Saliyo, da na sauran kasashe daban daban dake nahiyar Afirka, sun halarci bikin CIIE na bana, inda suka samu damar nuna fasahohi, da kayayyakinsu a wannan muhimmin dandali na kasa da kasa. Ya ce, “Bikin CIIE na kasar Sin ya ba mabambantan kasashe damar more ci gaban tattalin arzikinta, kana kasar ba za ta bar kowa a baya ba.” (Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaCGTNSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Bada Umarnin Sake Zabe A Wasu Sassan Jihar Kogi

Next Post

Majalisar Ɗinkin Duniya Da Tarayyar Turai Sun Miƙa Cibiyar Kula Da Matan Da Aka Ci Zarafinsu Ga Jihar Sokoto

Related

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

5 hours ago
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

6 hours ago
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

7 hours ago
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

8 hours ago
Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya
Daga Birnin Sin

Sin Da Myanmar Da Thailand Za Su Fatattaki Zambar Da Ake Yi Ta Hanyoyin Sadarwar Waya

9 hours ago
Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali
Daga Birnin Sin

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

1 day ago
Next Post
Majalisar Ɗinkin Duniya Da Tarayyar Turai Sun Miƙa Cibiyar Kula Da Matan Da Aka Ci Zarafinsu Ga Jihar Sokoto

Majalisar Ɗinkin Duniya Da Tarayyar Turai Sun Miƙa Cibiyar Kula Da Matan Da Aka Ci Zarafinsu Ga Jihar Sokoto

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.