ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisar Ɗinkin Duniya Da Tarayyar Turai Sun Miƙa Cibiyar Kula Da Matan Da Aka Ci Zarafinsu Ga Jihar Sokoto

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
Sokoto

Yayin da aka kammala aikin shirin kawo karshen cin zarafin mata na Kungiyar Tarayya Turai (EU) da Majalisar Dinkin Duniya tare da mikawa ga masu ruwa da tsaki, Gwamnan Jihar Sokoto, Dr Ahmed Aliyu, ya bayyana cewa bisa tallafin shirin, gwamnatin jihar ta inganta kula da wadanda suka tsira daga Cin Zarafi na Jinsi (SGBV) a cikin jihar.

“Mun inganta ayyukan kula da waɗanda suka tsira daga cin zarafi na Jima’i saboda bambancin jinsi (SGBV) kuma mun tabbatar da cewa mata da ‘yan mata sun sami damar samun kulawar da suke buƙata don sake gina rayuwarsu.” Ya bayyana hakan ne a wajen taron kammala shirin tare da mika cibiyar da aka samar ga Gwamnatin Jihar Sokoto, a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, a dakin taro na kasa da kasa da ke Sokoto.

  • Mata A Nemi Sana’a Kuma A Yi Addu’a – Asma’u Kabir
  • Dino Melaye Ya Lashe Akwatin Zabensa A Kogi

Gwamnan wanda ya samu wakilcin shugaban ma’aikatansa, Alhaji Aliyu Dikko, ya jaddada cewa “jihar ta yi namijin kokari wajen tabbatar da cewa mata da ‘yan mata sun samu kulawar da ta dace, tare da saukaka yunkurin farfadowa don sake gina rayuwarsu bayan da suka tsallaka siradi.

ADVERTISEMENT

Ya nanata kudurin jihar na kawar da cin zarafi da munanan ayyuka da ake yi wa mata da ‘yan mata, ya kuma jaddada gagarumin ci gaban da aka samu ta hanyar shirin mai lakabin ‘Spotlight Initiative’, wanda ya kasance wani cikakken shiri da aka tsara don tabbatar da cewa kowace mace walau babba ko yarinya za ta iya rayuwa a Jihar Sokoto ba tare da fuskantar wani tashin hankali da abubuwa na cin zarafi ba.

“Gwamnati ta himmatu wajen samar da dokoki da tsare-tsare da za su kare mata da ‘yan mata, tare da samar da yanayin da zai tabbatar da yin hukunci da adalci ga wadanda suka tsira daga cin zarafin mata a Jihar Sakkwato.” Ya bayyana.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Sokoto

Babban jami’in kula da kananan yara na Asusun UNICEF, Ibrahim Sesay, wanda ya wakilci Majalisar Dinkin Duniya a wajen taron ya ce, “A cikin shekaru biyar da suka gabata, tare da hadin gwiwar gwamnatin Jihar Sokoto, shirin na ‘Spotlight Initiative’ ya samu gagarumar nasara wajen magance matsalolin da suka shafi cin zarafin mata (GBV) da sauran munanan dabi’u da miyagu ke aikatawa a kan mata manya da yara.”

Ya bayyana wasu muhimman nasarorin da shirin ya samu kuma da suka hada da: samar da dokar kariya ga yara, da kafa Cibiyar Kula da Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafi (GBV), da yaye sama da mata 9,000 da aka koyar a karkashin shirin ilimi na musamman da aka tsara ga wadanda ba su yi karatu ba.

Sesay ya jaddada yawaitar abubuwan da ba su dace na zamantakewar al’umma da ake yi kamar aurar da ‘ya’ya mata da wuri, da kaciyar mata a Jihar Sakkwato, yayin da a cewarsa, har yanzu Nijeriya na ci gaba da fama da wadannan matsaloli da suka hada da aurar da ‘ya’ya mata kanana su miliyan 26 da wasu miliyan 19.9 da suka sha da kyar sanadin yi musu yankan gishiri.

“Wannan biki na rufewa ya zama kira ga masu ruwa da tsaki da su jajirce wajen ganin sun kare hakkin mata da yara a Jihar Sakkwato. Har ila yau, shirin yana bukatar gwamnati ta ware wani kaso na kudi tare da ba da fifiko ga kare yara da inganta daidaito tsakanin jinsi da karfafa mata.”

Sokoto

Kwamishiniyar kula da harkokin mata da yara na Jihar Sokoto, Hajiya Hadiza Ahmed Shagari ta bayyana cewa kare lafiyar mata da ‘yan mata na da matukar muhimmanci a Jihar Sokoto, don haka ne aka kafa wata cibiya mai suna ‘Nana Kadija Centre’.

Kwamishiniyar wadda babbar sakatariyar ma’aikatar, Hajiya Aisha Mohammed ta wakilta, ta bayyana cewa, “Mun samu nasara tare da yin aiki tare da dukkan abokan hulda na hukumomi, da kungiyoyi masu zaman kansu wadanda suka jajirce wajen gudanar da ayyuka daban-daban na magance cin zarafin mata da kuma kare yara a Jihar Sokoto.”

Alkalin Alkalan Jihar Sokoto, Hon. Mai shari’a Muhammad Sifawa, wacce Hajiya Mariya Haruna ta wakilta, ya bayyana jin dadinsa ga hukumar shari’a ta Jihar da kungiyar Tarayyar Turai da Majalisar Dinkin Duniya bisa goyon bayan da suka bayar tun bayan fara aikin a shekarar 2019.

Ya ce, “Ma’aikatar shari’a ta kuduri aniyar dagewa a kokarinta na ganin an gaggauta gudanar da shari’a kan laifukan da suka shafi cin zarafi na jinsi (GBV) da kuma munanan halaye, don tabbatar wa mata da ‘yan mata cewa akwai wani wuri mai aminci da za su iya kai kokensu duk lokacin da suke buƙatar hakan.”

Shirin na haɗin gwiwar ‘EU da UN Spotlight Initiative’, na da nufin kawar da cin zarafin mata da ‘yan mata da yaki da abubuwa masu cutarwa a Nijeriya, inda ya yi tasiri mai mahimmanci tun lokacin da aka kafa shi a 2019. An aiwatar da shirin cikin nasara a jihohi biyar: Adamawa, Kuros-Riba, Ebonyi, Legas, Sokoto, da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja.

Sokoto
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Alfanu Da Matsalolin Raba Wa Kishiyoyi Gida

Alfanu Da Matsalolin Raba Wa Kishiyoyi Gida

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.