Tambaya: Rahotanni na cewa, taron kolin rukunin G7 da ake gudanar da shi a Hiroshima na kasar Japan, ya fitar da hadaddiyar sanarwa da sauran takardu, inda aka zayyana batutuwan da suka shafi kasar Sin, tare da yin magana kan halin da ake ciki a mashigin tekun Taiwan. Shin Mene ne ra’ayin kasar Sin?
Amsa: Rukunin G7 na ikirarin kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya, amma suna daukar matakan kawo cikas ga zaman lafiya da kwanciyar hankalin shiyya-shiyya, da hana bunkasuwar sauran kasashe. G7 ta yi biris da muradun kasar Sin, tana yunkurin sarrafa batutuwan dake shafar kasar Sin, da shafa mata bakin fenti, da tsoma baki a harkokin cikin gidan Sin. Saboda haka kasar Sin tana matukar nuna rashin jin dadi da kin yarda da hakan. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp