Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya yi kira da a karfafa harkokin cinikayya da kasashen waje, bisa ruhin kirkire-kirkire da jan ragamar bangaren, tare da gaggauta samar da sabon karfin bude kofa.
Li Qiang ya bayyana haka ne lokacin da yake rangadi a lardin Fujian na kudu maso gabashin kasar Sin, daga ranar Talata zuwa jiya Alhamis.
- Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
- Gwamnoni Na Kamun Kafa A Wurin Tinubu Don Hana Bai Wa Kananan Hukumomi ‘Yanci
Firaministan ya yi kira da kada a yi kasa a gwiwa wajen fadada bude kofa da raya kasuwanni daban-daban da kuma kirkiro sabbin dabaru da hanyoyin kasuwanci.
Da yake bayyana kamfanoni masu zaman kansu a matsayin jigon kasar Sin na cinikayya da kasashen waje, Li Qiang ya ce ya kamata gwamnatoci a dukkan matakai, su yi kokarin samar da ingantattun manufofin tallafi da kyakkywan muhallin raya harkokin kasuwanci masu zaman kansu. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp