• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Ta Zama Jagora Mai Haskawa Duniya Sabuwar Hanyar Samun Zaman Lafiya Da Ci Gaba Ba Tare Da Nuna Fin Karfi Ba

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Sin

Yayin da ministan harkokin wajen Sin Wang Yi ke ziyara a kasar India, kasashen Sin da Indian sun amince da ci gaba da kyautata dangantakar dake tsakaninsu.

A cewar Wang Yi, a matsayinsu na manyan kasashe masu tasowa da jimilar al’ummarsu ta kai sama da biliyan 2.8, ya kamata kasashen biyu su zama misali ga kasashe masu tasowa wajen kara karfi ta hanyar hadin kai da bayar da gudunmawa ga cudanyar kasashe da rarrabuwar iko tsakanin kasa da kasa, maimakon kasancewa karkashin ikon wata kasa ko wasu ’yan tsirarun kasashe.

Tabbas tattaunawar da ake yi da tuntubar juna tsakanin India da Sin, abun yabawa ne saboda ya nuna wa duniya cewa, ba duka aka taru aka zama daya ba. Kuma manuniya ce cewa, akwai hanya mai bullewa ta samun zaman lafiya da kyautatuwar dangantaka ta hanyar tattaunawa, maimakon fin karfi da fito na fito.

Ta hanyar tattaunawa da tuntubar juna tsakanin kasashen biyu, tuni aka fara aiwatar da matsayar da shugabanninsu suka cimma tare da farfado da harkokin musaya da tattaunawa a tsakaninsu a dukkan matakai. Har ministan harkokin wajen India ya godewa kasar Sin bisa yadda ta saukakawa Indiyawa masu ziyarar ibada a yankin tsaunika da ma tabkunan lardin Xizang na kasar Sin. Wadannan sun nuna kyakkyawar niyyar kasashen biyu ta daidaita dadaddiyar huldar dake tsakaninsu.

Yayin da har yanzu wasu kasashe suka kasa hakura da tsohon ra’ayinsu na danniya da fin karfi, kasar Sin ta zama jagora mai haskawa kasashe masu tasowa wata hanya ta daban ta zaman lumana da samun ci gaba ba tare da nuna fin karfi ba. Haka kuma, ta kasance mai riko da hannayensu da kasancewa abun dogaro.

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Dawowar kyakkyawar alaka tsakanin Sin da Indiya, zai taimaka gaya wajen tabbatar da zaman lafiya a shiyyarsu. Kasancewarsu manyan abokan cinikayya kuma manyan kasashe masu tasowa haka ma kasashe mafiya yawan al’umma a duniya, ba su kadai da shiyyarsu ne za su amfana da kyautatuwar dangatakar ba, za ta bada gaggarumar gudunmawa ga ci gaban duniya ta fuskar tattalin arziki da zamantakewa da zaman lafiya, tare da zama misalin zaman jituwa bisa aminci da hadin gwiwa a tsakanin makwabta. Tabbas ina da yakinin na gaba kadan, bisa namijin kokarin da Sin ke ci gaba da yi na kokarin samar da sulhu da zaman lafiya a siyasance, za a kai ga kawar da danniya da babakere da cin zali a duniya.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

October 24, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Next Post
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Lakabin “Sautin Zaman Lafiya” A Moscow

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Lakabin "Sautin Zaman Lafiya" A Moscow

LABARAI MASU NASABA

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

Gombe Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Rano Air Don Fara Jigila Tsakanin Abuja Zuwa Gombe

October 24, 2025
Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

Shugaban Kasar Sin Zai Halarci Taron APEC Da Ziyarar Aiki A Korea Ta Kudu

October 24, 2025
Irin Ministocin Da ‘Yan Nijeriya Ke Tsammani Daga Gwamnatin Tinubu

Tinubu Ya Sauya Hafsoshin Tsaron Nijeriya

October 24, 2025
Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

Ɗan’uwa Ya Kwaƙule Idanuwan Ƙanwarsa Don Yin Tsafin Neman Kuɗi A Bauchi

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025, Injiniya Abdullahi Sule

October 24, 2025
Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

Ƴansanda Sun Sake Kama Sowore Bayan An Bayar Da Belinsa

October 24, 2025

Gwarzon Gwamnan 2025 Sanata Uba Sani: Mai Haɗa Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

October 24, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Sheriff Oboreɓwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

October 24, 2025
An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

An Kafa Cibiyoyi 296 Na Koyon Fasahar Zamani A Faɗin Nijeriya

October 24, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

Ƴan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan INEC Uku Da Wasu

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.