• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashe 10 Da Ke Kan Gaba A Mallakar Ma’adanin Gwal A Afirka

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Kasashe 10 Da Ke Kan Gaba A Mallakar Ma’adanin Gwal A Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nahiyar Afirka ke a kan gaba a fadin duniya a mallakar ma’adanin gwal, kasashe da dama a Afrika na da ma’adanin gwal shifide a karkashin kasashen su inda masana suka kiyasta cewa akwai fiye da metreic tan 1000 na ma’adanin gwal a kasashen, wanda kuma hakan wata hanya ce na samun arzikin da zai iya jagorantar bunkasa tattalin arzikin nahiyar gaba daya.

Ma’adanin Gwal na da muhimmanci a fannin bunkasa kudaden Najiyar na kasashen waje, yana taimakawa wajen rage dogaro da karbar bashi daga kasashen waje yana kuma jawo masu zuba jari daga kasashen waje, haka kuma yana taimakawa wajen daidaita darajar takardun kudaden kasa.

  • Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari
  • Gidauniyar Ahmadu Bello Ta Gano Matsalolin Da Suka Addabi Ilimi A Arewa

Bayanai da suka fito daga wata kungiya mai zaman kanta da ake kira ‘Statista’ a binciken da ta gabatar a shekarar 2023, ta bayyana cewa, kasashen Afrika 10 da ke a kan gaba wajen mallakar ma’adanin Gwal sun hada da.

 

Algeria

Labarai Masu Nasaba

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Kasar Algeria ke a kan gaba a mallakin ma’adanin Gwal a fadin Afirka, inda aka tattabar da tana da Gwal da ya kai fiye da Metrik tan 174. Kasar ta fara cin cikakkiyar gajiyar ma’adanin Gwal din ne tun a shekarar 2000, an kuma kiyasta Gwal din da ke a karkashin kasa a kasar ya kai na Dala Biliyan 10.

 

Afrika ta Kudu

Kasar Afirka ta Kudu, ita ma na daga cikin kasashen Afirka da ke kan gaba a mallakar ma’adanin Gwal. Kasar na da fiye da Metrik Tan 125 wanda aka kiyasta ya kai na fiye da na Dala Biliyan 7.

 

Libiya

Kasar Libiya na da ma’adanin Gwal na fiye da Metrik Tan 117 wanda aka kuma kiyasta ya fi na Dala Biliyan 6.

An samu nasarar cin gajiyar ma’adanin Gwal a Libiya ne a zaman mulkin Marigayi Shugaba Gaddafi, amma tun bayan mutuwarsa da kuma yakin basasa da ta barke a shekarar 2011 ba a ci gaba da cin gajiyar ma’adanin Gwal din ba.

 

Misra

Kasar Misra na da ma’adanin Gwal fiye da Metric Tan 80.73 wanda aka kuma kiyasta ya kai na Dala Biliyan 4. Kasar ta samu karuwar ma’adanin a ‘yan shekarun nan, musamma a kan yadda take son ta canza akalar tattalin arzikinta da kuma kokarinta na rage dogaro ga kudaden ajiyarta na kasashen waje.

 

Marocco

Kasar Marocco na da fiye da Metrik Tan 22.12 na ma’adanin Gwal wanda aka kiyasta ya kai na Dala Biliyan 1. Kasar ta fara cin gajiyar ma’adanan Gwal dinta ne tun a shekarar 1970.

 

Nijeriya

Nijeriya na da fiye da Metrik Tan 21.37 na ma’adanin Gwal a karkashin kasa an kuma kiyasta ya kai na Dala Biliyan 1. An ci gaba da gano karin ma’adanin Gwal a sassan kasar a ‘yan shekarun nan, inda kasar ke neman ta kara hanyoyin samun kudaden shigarta don a rage dogaro da take yi a kan albarkatun man fetur.

 

Mauritius

Kasar Mauritius na da fiye da Metric Tan 12.44 na ma’adanin Gwal, kasar ta fara cin gajiyar ma’adanin Gwal din ne tun daga shekarar 1980, an kuma kiyasata Gwal din da kasar ta mallaka ya kai na Dala Miliyan 700.

 

Ghana

Ghana na da ma’adanin Gwal da aka kiyasta ya kai Metrik Tan an kuma kiyasata ya kai na Dala Miliyan 500. Kasar ta samu karin nasarar samun gano karin ma’adanin Gwal a ‘yan shekarun nan, tana hankoron kara bude hanyoyin samnun kudaden shiga ne don kawar da kai daga yadda take dogara da Koko, an kuma kiyasata ma’adanin Gwal din da ke shifide a kasar ya kai na Dala Miliyan 500.

 

Tunisia

Tunisia na da fiye da Metrik Tan 6.84 na ma’adanin gwal shinfide a cikin kasa an kuma kiyasata ya kai na Dala Miliyan 400, kasar tana cin gajiiyar ma’adanin ne tun daga shekarar 1970.

 

Mozambikue

Kasar Mozambikue na da mallakin ma’adanin Gwal na fiye da metrik Tan 3.94 wanda aka kiyasata ya kai na Dala Miliyan 200. Kasar ta kuma ci gaba da gano karin ma’adanin a cikin ‘yan shekarun da suka gabata, inda take kokarin bunkasa tattalin arzikinta tare da rage dogaro da tallafi daga kasashen duniya.

Yadda kasashen Afirka ke kokarin ganin sun ci gajiyar ma’adanin Gwal a wannan lokacin wani alama ne na hankoronsu na fadada tattalin arzikin kasashen su da kuma kokarin su na rage dogaro ga tallafi da basuka daga kasashen Turai. Gwal na iya zama wata garkuwa ga kasashen Afirka na daukaka tare da gogayya da kasashe Turai a fage tattalin arziki duniya.

Karuwa ma’adanin gwal a Afirka zai taimaka wajen bukasa tattalin arzikin nahiyar gaba daya zai kuma kai ga bukasa kudaden kasashen waje tare da rage dogaro daga tallifi daga kasashe masu bayar da tallafi a duniya. Abin da ya rage a nan shi ne yadda gwamnatocin kasasshe Afirka za su tabbatar da cin gajiyar tare da amfanin da abubuwan da ake samu wajen bunkasa rayuwar al’umma Afirka ba tare nuna banbanci ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Afirka Ta Kudu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Zan Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ba – Gwamna Lawal

Next Post

Alkaluman Awon Sauyin Tsadar Kayayyaki Da Na Hidimomi Na Kasar Sin Ba Su Sauya Ba A Watan Satumba

Related

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

2 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

3 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

6 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

9 hours ago
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

10 hours ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba
Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

11 hours ago
Next Post
Alkaluman Awon Sauyin Tsadar Kayayyaki Da Na Hidimomi Na Kasar Sin Ba Su Sauya Ba A Watan Satumba

Alkaluman Awon Sauyin Tsadar Kayayyaki Da Na Hidimomi Na Kasar Sin Ba Su Sauya Ba A Watan Satumba

LABARAI MASU NASABA

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

June 3, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

June 3, 2025
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

June 3, 2025
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

June 3, 2025
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.