ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashe 10 Da Ke Kan Gaba A Mallakar Ma’adanin Gwal A Afirka

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Gwal

Nahiyar Afirka ke a kan gaba a fadin duniya a mallakar ma’adanin gwal, kasashe da dama a Afrika na da ma’adanin gwal shifide a karkashin kasashen su inda masana suka kiyasta cewa akwai fiye da metreic tan 1000 na ma’adanin gwal a kasashen, wanda kuma hakan wata hanya ce na samun arzikin da zai iya jagorantar bunkasa tattalin arzikin nahiyar gaba daya.

Ma’adanin Gwal na da muhimmanci a fannin bunkasa kudaden Najiyar na kasashen waje, yana taimakawa wajen rage dogaro da karbar bashi daga kasashen waje yana kuma jawo masu zuba jari daga kasashen waje, haka kuma yana taimakawa wajen daidaita darajar takardun kudaden kasa.

  • Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari
  • Gidauniyar Ahmadu Bello Ta Gano Matsalolin Da Suka Addabi Ilimi A Arewa

Bayanai da suka fito daga wata kungiya mai zaman kanta da ake kira ‘Statista’ a binciken da ta gabatar a shekarar 2023, ta bayyana cewa, kasashen Afrika 10 da ke a kan gaba wajen mallakar ma’adanin Gwal sun hada da.

ADVERTISEMENT

 

Algeria

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Yi Zargin Ana Shirin Hana ADC Shiga Zaɓen 2027

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

Kasar Algeria ke a kan gaba a mallakin ma’adanin Gwal a fadin Afirka, inda aka tattabar da tana da Gwal da ya kai fiye da Metrik tan 174. Kasar ta fara cin cikakkiyar gajiyar ma’adanin Gwal din ne tun a shekarar 2000, an kuma kiyasta Gwal din da ke a karkashin kasa a kasar ya kai na Dala Biliyan 10.

 

Afrika ta Kudu

Kasar Afirka ta Kudu, ita ma na daga cikin kasashen Afirka da ke kan gaba a mallakar ma’adanin Gwal. Kasar na da fiye da Metrik Tan 125 wanda aka kiyasta ya kai na fiye da na Dala Biliyan 7.

 

Libiya

Kasar Libiya na da ma’adanin Gwal na fiye da Metrik Tan 117 wanda aka kuma kiyasta ya fi na Dala Biliyan 6.

An samu nasarar cin gajiyar ma’adanin Gwal a Libiya ne a zaman mulkin Marigayi Shugaba Gaddafi, amma tun bayan mutuwarsa da kuma yakin basasa da ta barke a shekarar 2011 ba a ci gaba da cin gajiyar ma’adanin Gwal din ba.

 

Misra

Kasar Misra na da ma’adanin Gwal fiye da Metric Tan 80.73 wanda aka kuma kiyasta ya kai na Dala Biliyan 4. Kasar ta samu karuwar ma’adanin a ‘yan shekarun nan, musamma a kan yadda take son ta canza akalar tattalin arzikinta da kuma kokarinta na rage dogaro ga kudaden ajiyarta na kasashen waje.

 

Marocco

Kasar Marocco na da fiye da Metrik Tan 22.12 na ma’adanin Gwal wanda aka kiyasta ya kai na Dala Biliyan 1. Kasar ta fara cin gajiyar ma’adanan Gwal dinta ne tun a shekarar 1970.

 

Nijeriya

Nijeriya na da fiye da Metrik Tan 21.37 na ma’adanin Gwal a karkashin kasa an kuma kiyasta ya kai na Dala Biliyan 1. An ci gaba da gano karin ma’adanin Gwal a sassan kasar a ‘yan shekarun nan, inda kasar ke neman ta kara hanyoyin samun kudaden shigarta don a rage dogaro da take yi a kan albarkatun man fetur.

 

Mauritius

Kasar Mauritius na da fiye da Metric Tan 12.44 na ma’adanin Gwal, kasar ta fara cin gajiyar ma’adanin Gwal din ne tun daga shekarar 1980, an kuma kiyasata Gwal din da kasar ta mallaka ya kai na Dala Miliyan 700.

 

Ghana

Ghana na da ma’adanin Gwal da aka kiyasta ya kai Metrik Tan an kuma kiyasata ya kai na Dala Miliyan 500. Kasar ta samu karin nasarar samun gano karin ma’adanin Gwal a ‘yan shekarun nan, tana hankoron kara bude hanyoyin samnun kudaden shiga ne don kawar da kai daga yadda take dogara da Koko, an kuma kiyasata ma’adanin Gwal din da ke shifide a kasar ya kai na Dala Miliyan 500.

 

Tunisia

Tunisia na da fiye da Metrik Tan 6.84 na ma’adanin gwal shinfide a cikin kasa an kuma kiyasata ya kai na Dala Miliyan 400, kasar tana cin gajiiyar ma’adanin ne tun daga shekarar 1970.

 

Mozambikue

Kasar Mozambikue na da mallakin ma’adanin Gwal na fiye da metrik Tan 3.94 wanda aka kiyasata ya kai na Dala Miliyan 200. Kasar ta kuma ci gaba da gano karin ma’adanin a cikin ‘yan shekarun da suka gabata, inda take kokarin bunkasa tattalin arzikinta tare da rage dogaro da tallafi daga kasashen duniya.

Yadda kasashen Afirka ke kokarin ganin sun ci gajiyar ma’adanin Gwal a wannan lokacin wani alama ne na hankoronsu na fadada tattalin arzikin kasashen su da kuma kokarin su na rage dogaro ga tallafi da basuka daga kasashen Turai. Gwal na iya zama wata garkuwa ga kasashen Afirka na daukaka tare da gogayya da kasashe Turai a fage tattalin arziki duniya.

Karuwa ma’adanin gwal a Afirka zai taimaka wajen bukasa tattalin arzikin nahiyar gaba daya zai kuma kai ga bukasa kudaden kasashen waje tare da rage dogaro daga tallifi daga kasashe masu bayar da tallafi a duniya. Abin da ya rage a nan shi ne yadda gwamnatocin kasasshe Afirka za su tabbatar da cin gajiyar tare da amfanin da abubuwan da ake samu wajen bunkasa rayuwar al’umma Afirka ba tare nuna banbanci ba.

Gwal
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

Atiku Ya Yi Zargin Ana Shirin Hana ADC Shiga Zaɓen 2027
Manyan Labarai

Atiku Ya Yi Zargin Ana Shirin Hana ADC Shiga Zaɓen 2027

June 29, 2026
An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi
Labarai

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

June 29, 2026
Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina
Labarai

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Next Post
Alkaluman Awon Sauyin Tsadar Kayayyaki Da Na Hidimomi Na Kasar Sin Ba Su Sauya Ba A Watan Satumba

Alkaluman Awon Sauyin Tsadar Kayayyaki Da Na Hidimomi Na Kasar Sin Ba Su Sauya Ba A Watan Satumba

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Yi Zargin Ana Shirin Hana ADC Shiga Zaɓen 2027

Atiku Ya Yi Zargin Ana Shirin Hana ADC Shiga Zaɓen 2027

June 29, 2026
An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

An Fara Binciken Mutuwar Malamar Da Ƴan Uwan Ɗalibi Suka Kashe A Kogi

June 29, 2026
Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

Hatsarin Mota Ya Kashe Dalibin FUDMA, Wasu 17 Sun Jikkata A Katsina

June 29, 2026
Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.