ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashe 10 Da Ke Kan Gaba A Mallakar Ma’adanin Gwal A Afirka

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Gwal

Nahiyar Afirka ke a kan gaba a fadin duniya a mallakar ma’adanin gwal, kasashe da dama a Afrika na da ma’adanin gwal shifide a karkashin kasashen su inda masana suka kiyasta cewa akwai fiye da metreic tan 1000 na ma’adanin gwal a kasashen, wanda kuma hakan wata hanya ce na samun arzikin da zai iya jagorantar bunkasa tattalin arzikin nahiyar gaba daya.

Ma’adanin Gwal na da muhimmanci a fannin bunkasa kudaden Najiyar na kasashen waje, yana taimakawa wajen rage dogaro da karbar bashi daga kasashen waje yana kuma jawo masu zuba jari daga kasashen waje, haka kuma yana taimakawa wajen daidaita darajar takardun kudaden kasa.

  • Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari
  • Gidauniyar Ahmadu Bello Ta Gano Matsalolin Da Suka Addabi Ilimi A Arewa

Bayanai da suka fito daga wata kungiya mai zaman kanta da ake kira ‘Statista’ a binciken da ta gabatar a shekarar 2023, ta bayyana cewa, kasashen Afrika 10 da ke a kan gaba wajen mallakar ma’adanin Gwal sun hada da.

ADVERTISEMENT

 

Algeria

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Kasar Algeria ke a kan gaba a mallakin ma’adanin Gwal a fadin Afirka, inda aka tattabar da tana da Gwal da ya kai fiye da Metrik tan 174. Kasar ta fara cin cikakkiyar gajiyar ma’adanin Gwal din ne tun a shekarar 2000, an kuma kiyasta Gwal din da ke a karkashin kasa a kasar ya kai na Dala Biliyan 10.

 

Afrika ta Kudu

Kasar Afirka ta Kudu, ita ma na daga cikin kasashen Afirka da ke kan gaba a mallakar ma’adanin Gwal. Kasar na da fiye da Metrik Tan 125 wanda aka kiyasta ya kai na fiye da na Dala Biliyan 7.

 

Libiya

Kasar Libiya na da ma’adanin Gwal na fiye da Metrik Tan 117 wanda aka kuma kiyasta ya fi na Dala Biliyan 6.

An samu nasarar cin gajiyar ma’adanin Gwal a Libiya ne a zaman mulkin Marigayi Shugaba Gaddafi, amma tun bayan mutuwarsa da kuma yakin basasa da ta barke a shekarar 2011 ba a ci gaba da cin gajiyar ma’adanin Gwal din ba.

 

Misra

Kasar Misra na da ma’adanin Gwal fiye da Metric Tan 80.73 wanda aka kuma kiyasta ya kai na Dala Biliyan 4. Kasar ta samu karuwar ma’adanin a ‘yan shekarun nan, musamma a kan yadda take son ta canza akalar tattalin arzikinta da kuma kokarinta na rage dogaro ga kudaden ajiyarta na kasashen waje.

 

Marocco

Kasar Marocco na da fiye da Metrik Tan 22.12 na ma’adanin Gwal wanda aka kiyasta ya kai na Dala Biliyan 1. Kasar ta fara cin gajiyar ma’adanan Gwal dinta ne tun a shekarar 1970.

 

Nijeriya

Nijeriya na da fiye da Metrik Tan 21.37 na ma’adanin Gwal a karkashin kasa an kuma kiyasta ya kai na Dala Biliyan 1. An ci gaba da gano karin ma’adanin Gwal a sassan kasar a ‘yan shekarun nan, inda kasar ke neman ta kara hanyoyin samun kudaden shigarta don a rage dogaro da take yi a kan albarkatun man fetur.

 

Mauritius

Kasar Mauritius na da fiye da Metric Tan 12.44 na ma’adanin Gwal, kasar ta fara cin gajiyar ma’adanin Gwal din ne tun daga shekarar 1980, an kuma kiyasata Gwal din da kasar ta mallaka ya kai na Dala Miliyan 700.

 

Ghana

Ghana na da ma’adanin Gwal da aka kiyasta ya kai Metrik Tan an kuma kiyasata ya kai na Dala Miliyan 500. Kasar ta samu karin nasarar samun gano karin ma’adanin Gwal a ‘yan shekarun nan, tana hankoron kara bude hanyoyin samnun kudaden shiga ne don kawar da kai daga yadda take dogara da Koko, an kuma kiyasata ma’adanin Gwal din da ke shifide a kasar ya kai na Dala Miliyan 500.

 

Tunisia

Tunisia na da fiye da Metrik Tan 6.84 na ma’adanin gwal shinfide a cikin kasa an kuma kiyasata ya kai na Dala Miliyan 400, kasar tana cin gajiiyar ma’adanin ne tun daga shekarar 1970.

 

Mozambikue

Kasar Mozambikue na da mallakin ma’adanin Gwal na fiye da metrik Tan 3.94 wanda aka kiyasata ya kai na Dala Miliyan 200. Kasar ta kuma ci gaba da gano karin ma’adanin a cikin ‘yan shekarun da suka gabata, inda take kokarin bunkasa tattalin arzikinta tare da rage dogaro da tallafi daga kasashen duniya.

Yadda kasashen Afirka ke kokarin ganin sun ci gajiyar ma’adanin Gwal a wannan lokacin wani alama ne na hankoronsu na fadada tattalin arzikin kasashen su da kuma kokarin su na rage dogaro ga tallafi da basuka daga kasashen Turai. Gwal na iya zama wata garkuwa ga kasashen Afirka na daukaka tare da gogayya da kasashe Turai a fage tattalin arziki duniya.

Karuwa ma’adanin gwal a Afirka zai taimaka wajen bukasa tattalin arzikin nahiyar gaba daya zai kuma kai ga bukasa kudaden kasashen waje tare da rage dogaro daga tallifi daga kasashe masu bayar da tallafi a duniya. Abin da ya rage a nan shi ne yadda gwamnatocin kasasshe Afirka za su tabbatar da cin gajiyar tare da amfanin da abubuwan da ake samu wajen bunkasa rayuwar al’umma Afirka ba tare nuna banbanci ba.

Gwal
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Gwal
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gwal
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Alkaluman Awon Sauyin Tsadar Kayayyaki Da Na Hidimomi Na Kasar Sin Ba Su Sauya Ba A Watan Satumba

Alkaluman Awon Sauyin Tsadar Kayayyaki Da Na Hidimomi Na Kasar Sin Ba Su Sauya Ba A Watan Satumba

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Gwal

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Gwal

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.