ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 21, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashe 10 Da Ke Kan Gaba A Mallakar Ma’adanin Gwal A Afirka

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Gwal

Nahiyar Afirka ke a kan gaba a fadin duniya a mallakar ma’adanin gwal, kasashe da dama a Afrika na da ma’adanin gwal shifide a karkashin kasashen su inda masana suka kiyasta cewa akwai fiye da metreic tan 1000 na ma’adanin gwal a kasashen, wanda kuma hakan wata hanya ce na samun arzikin da zai iya jagorantar bunkasa tattalin arzikin nahiyar gaba daya.

Ma’adanin Gwal na da muhimmanci a fannin bunkasa kudaden Najiyar na kasashen waje, yana taimakawa wajen rage dogaro da karbar bashi daga kasashen waje yana kuma jawo masu zuba jari daga kasashen waje, haka kuma yana taimakawa wajen daidaita darajar takardun kudaden kasa.

  • Nijeriya Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur A 2024 —Kyari
  • Gidauniyar Ahmadu Bello Ta Gano Matsalolin Da Suka Addabi Ilimi A Arewa

Bayanai da suka fito daga wata kungiya mai zaman kanta da ake kira ‘Statista’ a binciken da ta gabatar a shekarar 2023, ta bayyana cewa, kasashen Afrika 10 da ke a kan gaba wajen mallakar ma’adanin Gwal sun hada da.

ADVERTISEMENT

 

Algeria

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

Kasar Algeria ke a kan gaba a mallakin ma’adanin Gwal a fadin Afirka, inda aka tattabar da tana da Gwal da ya kai fiye da Metrik tan 174. Kasar ta fara cin cikakkiyar gajiyar ma’adanin Gwal din ne tun a shekarar 2000, an kuma kiyasta Gwal din da ke a karkashin kasa a kasar ya kai na Dala Biliyan 10.

 

Afrika ta Kudu

Kasar Afirka ta Kudu, ita ma na daga cikin kasashen Afirka da ke kan gaba a mallakar ma’adanin Gwal. Kasar na da fiye da Metrik Tan 125 wanda aka kiyasta ya kai na fiye da na Dala Biliyan 7.

 

Libiya

Kasar Libiya na da ma’adanin Gwal na fiye da Metrik Tan 117 wanda aka kuma kiyasta ya fi na Dala Biliyan 6.

An samu nasarar cin gajiyar ma’adanin Gwal a Libiya ne a zaman mulkin Marigayi Shugaba Gaddafi, amma tun bayan mutuwarsa da kuma yakin basasa da ta barke a shekarar 2011 ba a ci gaba da cin gajiyar ma’adanin Gwal din ba.

 

Misra

Kasar Misra na da ma’adanin Gwal fiye da Metric Tan 80.73 wanda aka kuma kiyasta ya kai na Dala Biliyan 4. Kasar ta samu karuwar ma’adanin a ‘yan shekarun nan, musamma a kan yadda take son ta canza akalar tattalin arzikinta da kuma kokarinta na rage dogaro ga kudaden ajiyarta na kasashen waje.

 

Marocco

Kasar Marocco na da fiye da Metrik Tan 22.12 na ma’adanin Gwal wanda aka kiyasta ya kai na Dala Biliyan 1. Kasar ta fara cin gajiyar ma’adanan Gwal dinta ne tun a shekarar 1970.

 

Nijeriya

Nijeriya na da fiye da Metrik Tan 21.37 na ma’adanin Gwal a karkashin kasa an kuma kiyasta ya kai na Dala Biliyan 1. An ci gaba da gano karin ma’adanin Gwal a sassan kasar a ‘yan shekarun nan, inda kasar ke neman ta kara hanyoyin samun kudaden shigarta don a rage dogaro da take yi a kan albarkatun man fetur.

 

Mauritius

Kasar Mauritius na da fiye da Metric Tan 12.44 na ma’adanin Gwal, kasar ta fara cin gajiyar ma’adanin Gwal din ne tun daga shekarar 1980, an kuma kiyasata Gwal din da kasar ta mallaka ya kai na Dala Miliyan 700.

 

Ghana

Ghana na da ma’adanin Gwal da aka kiyasta ya kai Metrik Tan an kuma kiyasata ya kai na Dala Miliyan 500. Kasar ta samu karin nasarar samun gano karin ma’adanin Gwal a ‘yan shekarun nan, tana hankoron kara bude hanyoyin samnun kudaden shiga ne don kawar da kai daga yadda take dogara da Koko, an kuma kiyasata ma’adanin Gwal din da ke shifide a kasar ya kai na Dala Miliyan 500.

 

Tunisia

Tunisia na da fiye da Metrik Tan 6.84 na ma’adanin gwal shinfide a cikin kasa an kuma kiyasata ya kai na Dala Miliyan 400, kasar tana cin gajiiyar ma’adanin ne tun daga shekarar 1970.

 

Mozambikue

Kasar Mozambikue na da mallakin ma’adanin Gwal na fiye da metrik Tan 3.94 wanda aka kiyasata ya kai na Dala Miliyan 200. Kasar ta kuma ci gaba da gano karin ma’adanin a cikin ‘yan shekarun da suka gabata, inda take kokarin bunkasa tattalin arzikinta tare da rage dogaro da tallafi daga kasashen duniya.

Yadda kasashen Afirka ke kokarin ganin sun ci gajiyar ma’adanin Gwal a wannan lokacin wani alama ne na hankoronsu na fadada tattalin arzikin kasashen su da kuma kokarin su na rage dogaro ga tallafi da basuka daga kasashen Turai. Gwal na iya zama wata garkuwa ga kasashen Afirka na daukaka tare da gogayya da kasashe Turai a fage tattalin arziki duniya.

Karuwa ma’adanin gwal a Afirka zai taimaka wajen bukasa tattalin arzikin nahiyar gaba daya zai kuma kai ga bukasa kudaden kasashen waje tare da rage dogaro daga tallifi daga kasashe masu bayar da tallafi a duniya. Abin da ya rage a nan shi ne yadda gwamnatocin kasasshe Afirka za su tabbatar da cin gajiyar tare da amfanin da abubuwan da ake samu wajen bunkasa rayuwar al’umma Afirka ba tare nuna banbanci ba.

Gwal
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

MASU ALAKA

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir
Labarai

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

July 20, 2026
Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi
Labarai

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

July 20, 2026
Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu
Manyan Labarai

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Next Post
Alkaluman Awon Sauyin Tsadar Kayayyaki Da Na Hidimomi Na Kasar Sin Ba Su Sauya Ba A Watan Satumba

Alkaluman Awon Sauyin Tsadar Kayayyaki Da Na Hidimomi Na Kasar Sin Ba Su Sauya Ba A Watan Satumba

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

Sin Da Amurka Na Tuntubar Juna Game Da Inganta Mu’amalar Shugabanninsu A Bana

July 20, 2026
Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

Wang Yi: Kasar Sin Na Matukar Goyon Bayan Manufofin MDD

July 20, 2026
Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

Mayar Da Muradun Jama’a A Gaban Komai: Daga Hikimar Da Aka Gada Tsawon Dubban Shekaru Zuwa Akidar Zamani

July 20, 2026
NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

NAFDAC Ta Kama Jabun Giya, Gurbataccen Abinci Da Motocin Man Kalanzir

July 20, 2026
Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

Karfin Sin A Bangaren AI Ya Samarwa Kasashe Masu Tasowa Damarmakin Cin Gajiyar Fasahar

July 20, 2026
Sin Ta Zamo Kan Gaba A Duniya A Fannin Kirar Mutum-Mutumin Inji

Sin Ta Zamo Kan Gaba A Duniya A Fannin Kirar Mutum-Mutumin Inji

July 20, 2026
Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

Shari’ar Malami Ba Za Ta Dakatar Da Burinsa Na Gwamna Ba, Inji Jam’iyyar ADC Ta Kebbi

July 20, 2026
Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

Kimi K3 Ya Bayyana Yunkurin Sin Na Raya Fasahar AI A Bayyane Ta Yadda Kowa Zai Amfana

July 20, 2026
Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

Kwamandojin Kungiyar Ansaru Biyu Sun Amsa Laifin Garkuwa Da Mutane A Kotu

July 20, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin A Saliyo Ta Fara Horar Da Ma’aikatan Jinya Dabarun Likitancin Gargajiya Na Sin

July 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.