• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi

by Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da samun gagarumar nasara a fannin ilimi, inda sama da kashi 67 cikin 100 na dalibanta suka samu sakamako mai daraja ta biyar (C5) zuwa sama a jarrabawar kammala sakandare ta yammacin Afirka (WASSCE).

 

Kwamishinan Ilimi na Jihar, Farfesa Muhammad Sani Bello ne ya bayyana haka a taron kwana daya da hukumar tabbatar da ingancin makarantu ta jihar (KSSQA) ta shirya mai taken “Quality Assurance in Education: Summit for Best Practices”.

  • Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo
  • Karin Farashin Man Fetur: Ko Tinubu Zai Saurari Muryar Talaka?

Da yake zantawa da manema labarai, Farfesa Bello ya ce, wannan gagarumar nasara da aka samu, ta nuna irin hoɓɓasa da gwamnatin Gwamna Uba Sani ke yi a ɓangaren ilimi, da nufin daukaka darajar ilimi a jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Farfesa Bello ya yi nuni da cewa, “Kaduna ta himmatu wajen ganin cewa, ba wai kawai samun ilimi ba, har ma da tabbatar da dalibai sun kammala karatunsu da sakamako mai kyau. Mun riga mun ga gagarumar nasara, kuma muna fata wannan nasarar za ta ci gaba”

 

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa, tsarin ilimin jihar nan ba da jimawa ba zai zama na daya a Nijeriya wajen bayar da ilimi. Kwamishinan ya bukaci sauran hukumomi da su yi koyi da hukumar tabbatar da ingancin ilimi wajen aiwatar da dabarun kula da ingancin ilimi.

 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, Farfesa Usman Abubakar Zaria, babban darakta a hukumar KSSQA, ya bayyana matakai daban-daban da aka dauka na karfafa matakan ilimi a makarantun gwamnati da masu zaman kansu. Ya jaddada cewa, dole ne makarantu masu zaman kansu su bi ka’idojin tabbatar da ingancin ilimi a jihar.

 

“Daya daga cikin manyan nasarorin da muka samu a karkashin Gwamna Uba Sani shi ne, daukakar darajarmu a wurin samun sakamakon jarabawar kammala sakandire ta WAEC daga kashi 54 zuwa kashi 67 cikin 100, kuma darajarmu ta tashi daga na 10 zuwa na 7 a fadin kasar nan. Mun kuma bullo da ingantattun tsarin tantance jabun sakamako ta hanyar amfani da na’urar (QR code) da kuma fitar da sabbin fasahohi, kamar na’urorin kwamfuta, don inganta koyo,” in ji Farfesa Zaria.

 

Da yake jawabi a kan matsalar rashin tsaro da ta addabi wasu sassan jihar, Farfesa Zaria, ya ce, duk da cewa a baya rashin tsaro ya yi tasiri wajen hana yara shiga makarantu, amma a baya-bayan nan an samu ci gaba a fannin tsaro a fadin jihar, wanda a halin yanzu kananan yara da suka shiga makarantun firamare sun kai kusan miliyan 1.8, wanda a shekarar baya aka samu kimanin yara miliyan 1.7


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo

Next Post

Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

8 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

10 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

12 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

12 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

15 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

17 hours ago
Next Post
Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.