ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashi 67 Cikin 100 Na Ɗaliban Kaduna Sun Samu Nasara A WAEC – Kwamishinan Ilimi

by Sulaiman
1 year ago
Kwamishinan Ilimi

Gwamnatin jihar Kaduna ta sanar da samun gagarumar nasara a fannin ilimi, inda sama da kashi 67 cikin 100 na dalibanta suka samu sakamako mai daraja ta biyar (C5) zuwa sama a jarrabawar kammala sakandare ta yammacin Afirka (WASSCE).

 

Kwamishinan Ilimi na Jihar, Farfesa Muhammad Sani Bello ne ya bayyana haka a taron kwana daya da hukumar tabbatar da ingancin makarantu ta jihar (KSSQA) ta shirya mai taken “Quality Assurance in Education: Summit for Best Practices”.

ADVERTISEMENT
  • Gidauniyar Buratai Ta Taya Giwa-Daramola Murnar Zama Shugaban Kungiyar Tseren Kwale-kwale Na Ondo
  • Karin Farashin Man Fetur: Ko Tinubu Zai Saurari Muryar Talaka?

Da yake zantawa da manema labarai, Farfesa Bello ya ce, wannan gagarumar nasara da aka samu, ta nuna irin hoɓɓasa da gwamnatin Gwamna Uba Sani ke yi a ɓangaren ilimi, da nufin daukaka darajar ilimi a jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Farfesa Bello ya yi nuni da cewa, “Kaduna ta himmatu wajen ganin cewa, ba wai kawai samun ilimi ba, har ma da tabbatar da dalibai sun kammala karatunsu da sakamako mai kyau. Mun riga mun ga gagarumar nasara, kuma muna fata wannan nasarar za ta ci gaba”

 

Ya bayyana kwarin gwiwar cewa, tsarin ilimin jihar nan ba da jimawa ba zai zama na daya a Nijeriya wajen bayar da ilimi. Kwamishinan ya bukaci sauran hukumomi da su yi koyi da hukumar tabbatar da ingancin ilimi wajen aiwatar da dabarun kula da ingancin ilimi.

 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai, Farfesa Usman Abubakar Zaria, babban darakta a hukumar KSSQA, ya bayyana matakai daban-daban da aka dauka na karfafa matakan ilimi a makarantun gwamnati da masu zaman kansu. Ya jaddada cewa, dole ne makarantu masu zaman kansu su bi ka’idojin tabbatar da ingancin ilimi a jihar.

 

“Daya daga cikin manyan nasarorin da muka samu a karkashin Gwamna Uba Sani shi ne, daukakar darajarmu a wurin samun sakamakon jarabawar kammala sakandire ta WAEC daga kashi 54 zuwa kashi 67 cikin 100, kuma darajarmu ta tashi daga na 10 zuwa na 7 a fadin kasar nan. Mun kuma bullo da ingantattun tsarin tantance jabun sakamako ta hanyar amfani da na’urar (QR code) da kuma fitar da sabbin fasahohi, kamar na’urorin kwamfuta, don inganta koyo,” in ji Farfesa Zaria.

 

Da yake jawabi a kan matsalar rashin tsaro da ta addabi wasu sassan jihar, Farfesa Zaria, ya ce, duk da cewa a baya rashin tsaro ya yi tasiri wajen hana yara shiga makarantu, amma a baya-bayan nan an samu ci gaba a fannin tsaro a fadin jihar, wanda a halin yanzu kananan yara da suka shiga makarantun firamare sun kai kusan miliyan 1.8, wanda a shekarar baya aka samu kimanin yara miliyan 1.7

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Next Post
Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

Xi Zai Halarci Taron Kolin BRICS Karo Na 16 A Rasha

LABARAI MASU NASABA

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025
Tinubu

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

Tsohon Firaministan Japan Ya Soki Kalaman Takaichi Dangane Da Batun Yankin Taiwan

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.