• English
  • Business News
Saturday, June 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashun Da Nijeriya Ke Fitarwa Ya Karu Daga Naira Biliyan 116 Zuwa 146.1

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Kashun Da Nijeriya Ke Fitarwa  Ya Karu Daga Naira Biliyan 116 Zuwa 146.1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kididdiga ta kasa (National Bureau of Statistics), ta shelanta fitar da kashu na kimanin naira biliyan 146.1 zuwa kasashen waje a cikin watanni shida kacal.

Rahotan ya bayyana cewa, kashun na kimanin naira biliyan 102.3; an fitar da shi ne zuwa Kasashen Kudancin Gabashin Asiya.
Adadin kashun da aka fitar a wata shida na shekarar 2023, ya haura wanda aka fitar a shekarar 2022 zuwa kasashen wajen na kimanin naira biliyan 116.

  • Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kama Barayin Mota 3 A Bauchi
  • Za A Binciki Yadda Aka Karkatar Da Tallafin Korona Naira Biliyan 183.9

Idan za a iya tunawa, Shugaban Cibiyar Habbaka Fita da Kaya Kasashen Waje (NEPC), Dakta Ezra Yakusak, a watan Afrilu ya bayyana cewa, Nijeriya ta fitar da kashu na kimanin naira biliyan 116, wanda ya yi daidai da Dalar Amurka miliyan 252 a shekarar 2022.

Shugaban ya kara da cewa, kididdiga ta bayyana fitar da wannan kashu a matsayin na biyar cikin albakatun kasa da ya fi kawo wa Nijeriya kudin shiga baya ga man fetir a shekarar 2022.

Har ila yau, Sakatare Janar na kungiyar masu harkokin kashun ta Nijeriya, Sotonye Anga ya bayyana cewa, kashi 90 cikin 100 na masu noman wannan kashu tare da fitar da shi zuwa kasashen waje, na fitar da shi ne tsuransa; wanda hakan ya sa ake ta faman tafka asara a duk yayin da aka zo fitar da shi zuwa kasashen na waje.

Labarai Masu Nasaba

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

“A duk yayin da muka fitar da tsuran kashu zuwa kasashen waje, kamar muna yin watsi da ayyukan yi ne ga matasanmu ko kuma muna samar wa wasu kasashe da ban ayyukan yi a lokaci guda.

Don haka, muke kira ga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki, su yi kokari wajen habbaka tare da gyara wannan masana’anta, domin ci gaban kasa da samar da ayyukan yi da kuma sauran masu aiwatar da wannan sana’a baki-daya,” a cewar tasa.

Haka zalika, Sakatare Janar din ya kara bayyana cewa, har yanzu Nijeriya ba ta iya sarrafa sama da kashi 10 cikin 100 na wannan kashu, shi yasa suke kira ga gwamnatin da ta himmatu wajen kokarin gyara tare da fara sarrafa ko da kashi 30 ko 50 ne cikin 100.

Sannan, idan har za a bai wa wannan masana’anta ta kashu kulawar da ta dace, ko shakka babu Nijeriya za ta iya samun kudin shiga da ya kai kimanin biliyan 30 zuwa 200 nan da shekaru biyar masu zuwa, wanda hakan zai ba wa masana’antar damar shiga cikin jerin sahun gaba na wadanda suka fi bai wa Nijeriya gudunmawa na kudin shiga, a cewar ta Anga.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kasashen ketareNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Daure Matashi Shekara 34 Bisa Laifin Garkuwa Da Mutane Da Fyade

Next Post

Batun Bude Iyakokin Nijeriya

Related

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

12 hours ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

7 days ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

7 days ago
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

2 weeks ago
Neja
Noma Da Kiwo

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

2 weeks ago
Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani
Noma Da Kiwo

Gwamna Zulum Ya Nemi A Zuba Hannun Jari A Harkar Noman Rani

3 weeks ago
Next Post
Batun Bude Iyakokin Nijeriya

Batun Bude Iyakokin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

June 20, 2025
Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

June 20, 2025
Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

June 20, 2025
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

June 20, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

June 20, 2025
Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici

Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici

June 20, 2025
Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

June 20, 2025
Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

June 20, 2025
Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

June 20, 2025
An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

June 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.