ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashun Da Nijeriya Ke Fitarwa Ya Karu Daga Naira Biliyan 116 Zuwa 146.1

by Abubakar Abba
2 years ago
Nijeriya

Hukumar Kididdiga ta kasa (National Bureau of Statistics), ta shelanta fitar da kashu na kimanin naira biliyan 146.1 zuwa kasashen waje a cikin watanni shida kacal.

Rahotan ya bayyana cewa, kashun na kimanin naira biliyan 102.3; an fitar da shi ne zuwa Kasashen Kudancin Gabashin Asiya.
Adadin kashun da aka fitar a wata shida na shekarar 2023, ya haura wanda aka fitar a shekarar 2022 zuwa kasashen wajen na kimanin naira biliyan 116.

  • Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kama Barayin Mota 3 A Bauchi
  • Za A Binciki Yadda Aka Karkatar Da Tallafin Korona Naira Biliyan 183.9

Idan za a iya tunawa, Shugaban Cibiyar Habbaka Fita da Kaya Kasashen Waje (NEPC), Dakta Ezra Yakusak, a watan Afrilu ya bayyana cewa, Nijeriya ta fitar da kashu na kimanin naira biliyan 116, wanda ya yi daidai da Dalar Amurka miliyan 252 a shekarar 2022.

ADVERTISEMENT

Shugaban ya kara da cewa, kididdiga ta bayyana fitar da wannan kashu a matsayin na biyar cikin albakatun kasa da ya fi kawo wa Nijeriya kudin shiga baya ga man fetir a shekarar 2022.

Har ila yau, Sakatare Janar na kungiyar masu harkokin kashun ta Nijeriya, Sotonye Anga ya bayyana cewa, kashi 90 cikin 100 na masu noman wannan kashu tare da fitar da shi zuwa kasashen waje, na fitar da shi ne tsuransa; wanda hakan ya sa ake ta faman tafka asara a duk yayin da aka zo fitar da shi zuwa kasashen na waje.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

“A duk yayin da muka fitar da tsuran kashu zuwa kasashen waje, kamar muna yin watsi da ayyukan yi ne ga matasanmu ko kuma muna samar wa wasu kasashe da ban ayyukan yi a lokaci guda.

Don haka, muke kira ga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki, su yi kokari wajen habbaka tare da gyara wannan masana’anta, domin ci gaban kasa da samar da ayyukan yi da kuma sauran masu aiwatar da wannan sana’a baki-daya,” a cewar tasa.

Haka zalika, Sakatare Janar din ya kara bayyana cewa, har yanzu Nijeriya ba ta iya sarrafa sama da kashi 10 cikin 100 na wannan kashu, shi yasa suke kira ga gwamnatin da ta himmatu wajen kokarin gyara tare da fara sarrafa ko da kashi 30 ko 50 ne cikin 100.

Sannan, idan har za a bai wa wannan masana’anta ta kashu kulawar da ta dace, ko shakka babu Nijeriya za ta iya samun kudin shiga da ya kai kimanin biliyan 30 zuwa 200 nan da shekaru biyar masu zuwa, wanda hakan zai ba wa masana’antar damar shiga cikin jerin sahun gaba na wadanda suka fi bai wa Nijeriya gudunmawa na kudin shiga, a cewar ta Anga.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima
Noma Da Kiwo

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Next Post
Batun Bude Iyakokin Nijeriya

Batun Bude Iyakokin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.