ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashun Da Nijeriya Ke Fitarwa Ya Karu Daga Naira Biliyan 116 Zuwa 146.1

by Abubakar Abba
3 years ago
Nijeriya

Hukumar Kididdiga ta kasa (National Bureau of Statistics), ta shelanta fitar da kashu na kimanin naira biliyan 146.1 zuwa kasashen waje a cikin watanni shida kacal.

Rahotan ya bayyana cewa, kashun na kimanin naira biliyan 102.3; an fitar da shi ne zuwa Kasashen Kudancin Gabashin Asiya.
Adadin kashun da aka fitar a wata shida na shekarar 2023, ya haura wanda aka fitar a shekarar 2022 zuwa kasashen wajen na kimanin naira biliyan 116.

  • Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kama Barayin Mota 3 A Bauchi
  • Za A Binciki Yadda Aka Karkatar Da Tallafin Korona Naira Biliyan 183.9

Idan za a iya tunawa, Shugaban Cibiyar Habbaka Fita da Kaya Kasashen Waje (NEPC), Dakta Ezra Yakusak, a watan Afrilu ya bayyana cewa, Nijeriya ta fitar da kashu na kimanin naira biliyan 116, wanda ya yi daidai da Dalar Amurka miliyan 252 a shekarar 2022.

ADVERTISEMENT

Shugaban ya kara da cewa, kididdiga ta bayyana fitar da wannan kashu a matsayin na biyar cikin albakatun kasa da ya fi kawo wa Nijeriya kudin shiga baya ga man fetir a shekarar 2022.

Har ila yau, Sakatare Janar na kungiyar masu harkokin kashun ta Nijeriya, Sotonye Anga ya bayyana cewa, kashi 90 cikin 100 na masu noman wannan kashu tare da fitar da shi zuwa kasashen waje, na fitar da shi ne tsuransa; wanda hakan ya sa ake ta faman tafka asara a duk yayin da aka zo fitar da shi zuwa kasashen na waje.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

“A duk yayin da muka fitar da tsuran kashu zuwa kasashen waje, kamar muna yin watsi da ayyukan yi ne ga matasanmu ko kuma muna samar wa wasu kasashe da ban ayyukan yi a lokaci guda.

Don haka, muke kira ga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki, su yi kokari wajen habbaka tare da gyara wannan masana’anta, domin ci gaban kasa da samar da ayyukan yi da kuma sauran masu aiwatar da wannan sana’a baki-daya,” a cewar tasa.

Haka zalika, Sakatare Janar din ya kara bayyana cewa, har yanzu Nijeriya ba ta iya sarrafa sama da kashi 10 cikin 100 na wannan kashu, shi yasa suke kira ga gwamnatin da ta himmatu wajen kokarin gyara tare da fara sarrafa ko da kashi 30 ko 50 ne cikin 100.

Sannan, idan har za a bai wa wannan masana’anta ta kashu kulawar da ta dace, ko shakka babu Nijeriya za ta iya samun kudin shiga da ya kai kimanin biliyan 30 zuwa 200 nan da shekaru biyar masu zuwa, wanda hakan zai ba wa masana’antar damar shiga cikin jerin sahun gaba na wadanda suka fi bai wa Nijeriya gudunmawa na kudin shiga, a cewar ta Anga.

Nijeriya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Batun Bude Iyakokin Nijeriya

Batun Bude Iyakokin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.