ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kashun Da Nijeriya Ke Fitarwa Ya Karu Daga Naira Biliyan 116 Zuwa 146.1

by Abubakar Abba
3 years ago
Nijeriya

Hukumar Kididdiga ta kasa (National Bureau of Statistics), ta shelanta fitar da kashu na kimanin naira biliyan 146.1 zuwa kasashen waje a cikin watanni shida kacal.

Rahotan ya bayyana cewa, kashun na kimanin naira biliyan 102.3; an fitar da shi ne zuwa Kasashen Kudancin Gabashin Asiya.
Adadin kashun da aka fitar a wata shida na shekarar 2023, ya haura wanda aka fitar a shekarar 2022 zuwa kasashen wajen na kimanin naira biliyan 116.

  • Sojoji Sun Kashe Dan Bindiga, Sun Kama Barayin Mota 3 A Bauchi
  • Za A Binciki Yadda Aka Karkatar Da Tallafin Korona Naira Biliyan 183.9

Idan za a iya tunawa, Shugaban Cibiyar Habbaka Fita da Kaya Kasashen Waje (NEPC), Dakta Ezra Yakusak, a watan Afrilu ya bayyana cewa, Nijeriya ta fitar da kashu na kimanin naira biliyan 116, wanda ya yi daidai da Dalar Amurka miliyan 252 a shekarar 2022.

ADVERTISEMENT

Shugaban ya kara da cewa, kididdiga ta bayyana fitar da wannan kashu a matsayin na biyar cikin albakatun kasa da ya fi kawo wa Nijeriya kudin shiga baya ga man fetir a shekarar 2022.

Har ila yau, Sakatare Janar na kungiyar masu harkokin kashun ta Nijeriya, Sotonye Anga ya bayyana cewa, kashi 90 cikin 100 na masu noman wannan kashu tare da fitar da shi zuwa kasashen waje, na fitar da shi ne tsuransa; wanda hakan ya sa ake ta faman tafka asara a duk yayin da aka zo fitar da shi zuwa kasashen na waje.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

“A duk yayin da muka fitar da tsuran kashu zuwa kasashen waje, kamar muna yin watsi da ayyukan yi ne ga matasanmu ko kuma muna samar wa wasu kasashe da ban ayyukan yi a lokaci guda.

Don haka, muke kira ga gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki, su yi kokari wajen habbaka tare da gyara wannan masana’anta, domin ci gaban kasa da samar da ayyukan yi da kuma sauran masu aiwatar da wannan sana’a baki-daya,” a cewar tasa.

Haka zalika, Sakatare Janar din ya kara bayyana cewa, har yanzu Nijeriya ba ta iya sarrafa sama da kashi 10 cikin 100 na wannan kashu, shi yasa suke kira ga gwamnatin da ta himmatu wajen kokarin gyara tare da fara sarrafa ko da kashi 30 ko 50 ne cikin 100.

Sannan, idan har za a bai wa wannan masana’anta ta kashu kulawar da ta dace, ko shakka babu Nijeriya za ta iya samun kudin shiga da ya kai kimanin biliyan 30 zuwa 200 nan da shekaru biyar masu zuwa, wanda hakan zai ba wa masana’antar damar shiga cikin jerin sahun gaba na wadanda suka fi bai wa Nijeriya gudunmawa na kudin shiga, a cewar ta Anga.

Nijeriya
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Batun Bude Iyakokin Nijeriya

Batun Bude Iyakokin Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.