Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Killace Daura: Dole Mutane Su Fito Neman Abinci Idan Ba So Ake Su Mutu Ba -Hon Sirika

by
2 years ago
in LABARAI
2 min read
Killace Daura: Dole Mutane Su Fito Neman Abinci Idan Ba So Ake Su Mutu Ba -Hon Sirika
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Kwamishinan yada labarai na jihar Katsina kuma shugaban kwamitin wayar da kan jama’a akan matsalar Cobid 19 Hon. Abdulkarin Yahaya Sirika ya bayyana cewa dole mutane Daura su fita sayan abinci ko neman magani idan ba su ake su mutu ba.

Duk da dokar ta bacin da aka kakabawa Daura, amma jama’a na cigaba da yin hada-hadarsu, shin ko Hon. Kwamishina ya ga wadannan mutane tunda ya zagaya cikin garin Daura?, sai ya ce shi kam bai ga kowa ba, kuma ko da an ga mutun bai wuce wanda zai je sayan magani ko abinci ba, saboda an ware wasu wurare domin yin haka.

Shugaban kwamitin yana wannan magana ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Daura lokacin da muka kai ziyarar gani da akan irin abubuwan da suke faruwa a garin na Daura dangane da dokar tana shiga da fita da gwamnati jihar Katsina ta sanya a ranar asabar din da ta gabata.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

Hon. Sirika ya kara da cewa duk abinda aka ga gwamnatin ta yi to ta yi ne domin jama’a saboda haka wannan doka ta dan wani lokaci ce, kuma da zaran an samu abinda ake so, wannan abu zai kwaranye kamar ba a yi.

“Kuma abinda muke cewa shi ne, gwamnatin na nan tana kokarin wajan ganin ta tallafawa mutanen garin Daura saboda yanayin da aka shiga ciki, saboda haka muna kira ga masu kudin Daura da ‘yan kasuwa da ‘yan siyasa da su taimakawa mutane Daura domin aikin ba na gwamnati bane kadai” inji

A cewarsa tallafin da gwamnatin jihar Katsina zata bada ba zai dauki wani lokaci ba, saboda haka jama’a su kara hakuri, nan gaba kadan za su ga wannan sako na bangaran gwamnatin jihar Katsina.

Da yawan jama’ar da muka tattauna da su, sun koka akan yadda aka hana su fita kuma babu wani taimako da aka yi masu duk da kasancewar mafiyawan mutane sai sun fita suke neman abinda za su sanya a bakin sati.

Haka kuma mun lura da cewa jami’an tsaro ba su takurawa kowa ba, domin jama’a na cigaba da yin huldarsu a kofar gidajansu, wasu kuma na ta yi akan titi wasu kuma na zaune a majalisa a ya yin da wasu ke cikin gidajansu domin bin doka da oda.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Wasu Dabaru Uku Da Amurka Take Amfini Da Su Domin Bata Sunan Kasar Sin

Next Post

Hukumar Shige Da Fice Ta Tarbi ‘Yan Nijeriya 23 Da Suka Dawo Daga Togo

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

by
3 hours ago
0

...

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

by
15 hours ago
0

...

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

by Abdulrazaq Yahuza Jere
24 hours ago
0

...

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

by Abubakar Abba
2 days ago
0

...

Next Post
Hukumar Shige Da Fice Ta Tarbi ‘Yan Nijeriya 23 Da Suka Dawo Daga Togo

Hukumar Shige Da Fice Ta Tarbi 'Yan Nijeriya 23 Da Suka Dawo Daga Togo

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: