• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiraye-Kirayen Neman Gwamnatin Tarayya Ta Karbi Wasu Filayen Jiragen Sama Na Jihohi

by Leadership Hausa
3 years ago
in Rahotonni
0
Kiraye-Kirayen Neman Gwamnatin Tarayya Ta Karbi Wasu Filayen Jiragen Sama Na Jihohi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jihohi uku, da suka hada da Ebonyi, Gombe da kuma Nasarawa sun mika bukatar gwamnatin tarayya ta karbi harkokin gudanar da filayen jiragen saman jihohin su, bukatar da gwamnati ta amince da ita. Wannan kuma yana nufin cewa, a ‘yan kwanaki masu zuwa dole gwamnatin tarayya ta amayo wasu biliyoyin nairori don mayar wa da gwamnatocin wadannan jihohin, misali a nan shi ne gwamnatin Jihar Nasarawa ta mika bukatar Naira Biliyan 10 ga gwamnatin tarayya na karbar ragamar filin jiragen sama dana daukar manya kaya na garin Lafia da ke Jihar Nasarawar.

Babban abin da ya kamata a fahimta a nan shi ne wadannanfilayen jiragen sama da aka gina a jihohin nan uku duk an yi sune da manufar siyasa kawai ba wai don wani buri na bunkasar tattalin arziki ba.

  • Tsare-tsaren CBN Don Samar Da Kyakkyawar Alkibla Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Mutane 8 Sun Mutu, 2 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi 

Muna wannan bayanin ne don tunda farko akwai filayen jiragen sama da al’ummar wadannan jihohin za su iya amfani da su ba tare da wata matsala ba, misali, jihar Ebonyi za ta iya a cikin sauki da filin jiragen sama na garin Inugu; Jihar Gombe za ta iya amfani da na garin Bauchi yayin da filin jirgin sama na jihar Benuwai zai iya zama abin amfani ga al’umma JIhar Nasarawa.

Duk da cewa, ana sa ran filayen jiragen saman su samar da kudin shiga amma bincikenmu ya nuna cewa, cikin filayen jiragen sama 22 da muke da su a Nijeriya filayen jirgin sama na Legas, Fatakwal, Kano da kuma Abuja ne kawai kuma wadanda dukkansu hukumar Kula da filayen jiragen saman ta Nijeriya ke kula da su kadai ke samar da kudin shigar da za a iya magana a kai.

A ra’ayin wannan jaridar, shawarar wasu gwamnonin jihohi ta samar da filayen jiragen sama abu ne da ba zai haifar da da mai ido ba. Yawanci su suna gina filayen ne don cimma wani buri na kashin kansu. Wanann kuma abin takaici ne in har muka lura da cewa, gina filin Jirgin sama abu ne da yake bukatar dinbin kudade masu yawan gaske.

Labarai Masu Nasaba

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

Mai zai sa jihar da take rarrafe tare da neman kudaden gudanar da ayyukanta za ta fara kaddamar da gina filin Jirgin sama tun da farko? Wannan kamar an yi ne kawai don biyan bukatar wasu kalilan daga cikin al’ummar jihar masu hannun da shuni, maimakon a karkatar da kudaden wajen samar da hanyoyin warware matsalolin da al’umma ke fuskanta na rashin Ruwan sha da hanyoyi da wutar lanytar da sauran ababen more rayuwa da mafi yawan mutanen jihohin ke fuskanta.

A bayyana yake cewa, gwamnatin Jihar Ebonyi ta yanzu da gwamnatocin da suka shude a jihohin Gombe da Nasarawa ba su yi bincike na yadda kamata ba kafin su tsiri fara gina filayen jirgin sama a yankunan nasu, da gwamnatocin wadannan jihohin sun yi wannan bincike da basu kai yin haka ba don yin wannan aikin tamkar rashin sanin abin da ya kamata a muhimmantar da shi ne a rayuwar al’umma gaba daya.

Idan za a yi adalci ga GwamnaAbdullahi Sule da Gwamna Muhammadu Yahaya, wadanda suka gada Tsofaffin gwamnonin jihohin da suka hada da Umaru Tanko Al-Makura da Danjuma Goje sune suka kirkiri gina filayen jiragen saman a jihohin Nasarawa da Gombe.

Ana iya cewa, ba zai yiwu Gwamna Sule da Gwamna Yahaya, wadanda dukkan su ‘yan kasuwa ne su rungumi irin wannan harkar ta samar da filayen sama tun da farko ba.

Amma ga Gwamnan jihar Ebonyi, Dabe Umahi wannan kamar wani babbar rashinm muhimmantar da abin da al’umma ke bukata ne. Ba tare da la’akari da yadda jihar za ta fuskanci kula da filin jirgin sama ba kawai sai ya fada gina filin jirgin sama na kasa da kasa, sai kuma ga shi wai yana neman gwamnatin tarayya da ta karbi ragamar gudanar da filin jirgin, wanda ya gada tsohon gwamna Dakta Sam Egwu ya yi irin wannan kuskuren inda ya gina katafariyar cibiyar masana’antu a garin Abakaliki wadda al’umma suka rasa cikakken amfaninta.

Idan za a iya tunawa a shekarar da ta gabata ne Gwamna Umahi ya rubuta wa gwamnatin tarayya bukatar neman bashin Naira Biliyan 10 don sayen kayayyakin aiki na filin jirgin sama, yana mai cewa, da zarar an kamala aikin za su mika filin jirgin ne ga gwamnatin tarayya.

Kwanaki ne kuma Gwamna Umahi ya sanar da gina gidan gwamnatin jihar a kan kudi Naira Biliyan 1.2 a garin Abuja wannan ma wani aikin baban giwa ne.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, in har gwamnatin tarayya ta kuskura ta karbi ragamar wadannan filayen jiragen saman to kamar ta ba wasu jihohi damar shiga sahun irin wadannan aikin ne na baban giwa da ba zai yi wa al’umma amfanin komai ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Filin Jirgin SamaGwamnatin TarayyaGwamnoniHukunci
ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Yayin Da Yakin Neman Zaben 2023 Ya Kankama…

Related

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

4 days ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

5 days ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

7 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

2 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

2 weeks ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

2 weeks ago
Next Post
Shirin Twitter Space Na LEADERSHIP Hausa: Yadda ‘Yan Nijeriya Za Su Kauce Wa Komawa ‘Yar Gidan Jiya A Zaben 2023

Yayin Da Yakin Neman Zaben 2023 Ya Kankama…

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki

September 11, 2025
Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

Za A Gudanar Taron Tattaunawa Karo Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Nan Birnin Beijing

September 11, 2025
Shettima

Shettima Ya Bada Umarnin Gaggauta Raba Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Ƙananan Manoma 

September 11, 2025
An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

An Zabi Wuraren Ban Ruwa Hudu Na Kasar Sin Domin Shigar Da Su Jadawalin Wuraren Ban Ruwa Na Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

Rashin Tsaro: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jihar Kogi 

September 11, 2025
Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

Shawarar Jagorantar Harkokin Duniya: Mafitar Sin Ga Kasa Da Kasa

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.