• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Jami’an ‘Yansanda 229 A Cikin Wata 22 Babbar Musiba Ce Ga Kasa

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
Yansanda

Ga akasarin ‘yan Nijeriya rahoton da aka wallafa na kashe jami’ian ‘yan sanda 229 a cikin watanni 22, wani abin damuwa ne.

Wadannan alkalumman sun nuna yadda, aka samu raguwar jam’ian da ke rike da manyan mukamai da suka kai kaso goma a cikin wata.

  • Tallafin Wutar Lantarki Ya Kai Naira Biliyan 199.64 A Nijeriya – NERC
  • Yadda Ciniki Ya Habaka Tsakanin Babban Yankin Kasar Sin Da Yankin Macao A Fiye Da Shekaru 25

Wannan ta’addacin da aka yi wa wadannan ‘yan sandan da suka rasa rayukansu, babban abin damuwa ne, kuma abu ne, da ba za a lumunta ba, kuma dole ne, a gudanar da bincke, duk da cewa, duk wanda aka dauke shi aikin wanzar da tsaro, zai iya rasa ransa, ako wane lokaci.

Amma wannan zafin rashin na jami’an, duk da cewa, mutuwa wata aba ce, da ba za a iya kaucewa mata ba.

Wasu rahotannin sun bayyana cewa, adadin na wadannan mamatan ‘yan sandan, ko dai ‘yan bindiga daji, ‘yan bindiga, ‘yan kungiyar ta’addan Boko Haram, ‘yan kungiyar asiri da kuma masu fashi da makami ne, suka yi salar salwantar da rayukansu.

LABARAI MASU NASABA

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

Sun dai, rasa rayukansu ne, a yayin da suke kan gudanar da ayyukansu na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

Duba da wannan rahoton za a iya yin tunanin irin yawan ‘yan Nijeriya da ba su ji, ba su kuma gani ba, suka rasa nasu rayukan, duk a cikin wadannan watannin 22.

‘Yan Nijeriyar sun rasa rayukansu ne, ba wai domin sun aikata wani laifi ba, sai dai kawai, domin wasu ‘yan siyasa masu rike da madafun iko ne, ke shugabanta su, ba su dauki rayukansu a bakin komai ba.

A Nijeriya abin ba a boye yake ba, domin aikin na ‘yan sandan kasar tamkar sadaukar da rai ne, musamman ma da yadda suke yin artabu da miyagun masu aikata manyan laifuka a yayin gudanar da aikinsu.

Wani abin bakin ciki shi ne, a yayin artabun, miyagun sun kasance suna dauke da manyan makamai ne, da suka fi na ‘yan sandan, wanda a wani lokacin, hakan ke bai wa miyagun galaba, a kan ‘yan sandan a lokacin artabun.

Wannan jaridar ta dade tana maimaita maganar cewa, akwai matukar bukatar a wadata jami’an ‘yan sandan kasar nan, da manyan makamai, idan ka yi la’akari da irin hadarin da ke tattare da aikinsu.

Wani abin takaici shi ne, yadda mahukuntan ‘yan sanda a kasar, ba su bai wa ‘yan sanda wadatattun Albarusai, wanda kuma ake kakaba masu takunkumin dole ne, sai sun sanar da hukumomin ‘yan sandan, adadin Albarusan da suka yi amfan da su a yayin da suke gudanar da aikinsu, na kwantar da duk wata kura, da ta taso.

A rubuce yake a kasar nan cewa, a daukacin bangaren jami’an tsaron kasa, bagaren ‘yan sanda, sune koma baya wajen rashin kula da jin dadinsu da walwalarsu.

Wannan matsalar, ta kasance tana karya masu gwiwa wajen gudanar da aikinsu a cikin nuna kwarewa, domin yiwa alumma aiki yadda ya dace.

A wasu lokutan ma, sune suke sayawa kansu kaki da wasu manyan kayan aiki, domin kawai, su gudanar da aikisnu, na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan kasa.

Sai dai kuma, wannan ya tabbatar da maganar mu, duba da yadda ake wadata su da manyan makamai idan an tura zuwa wasu kasashe don tabbatar da zaman lafiya.

Kazalika, wani abin dubi shi ne, yadda ‘yan sandan suke gudanar da aikinsu, ba tare da suna da wata kwarewar kirki ba, koda yake, wasu na cewa, haka irin aikin nasu yake, amma mu ana nan, muna da jayya kan wannan ra’ayin, domin kuwa, ba irin aikin ‘yan sanda bane, a cikin tawargar su, su rinka farautar manyan masu aikita laifi, a cikin motocin su da suka riga suka tsufa ba.

Babban hatsari ne ga ‘yan sanda su fita gudana da aiki da Albarusan da aka kidaya masu, za su yi amfani da su ba.

Hakazalika, bama goyon bayan cewar da ake yi ‘yan sandan su kula da jin dadinsu da walwalarsu da kansu, domin kawai, Babban Sifeta Janar na ‘yan sanda ya amince masu su sanya kaki.

Dole, a a tabbatar da ana kula da sa kishin kasa, musamman a aiki irin na ‘yan sanda, duba da irin barazanar da suke fuskanta a yayin gudanar da aikinsu.

Suma ‘yan Adam ne, kamar kowanne dan kasa kuma suna da iyali da ‘yan uwa, da suka dogara a kansu.

Mun dade muna ankarar da hukumomin tsaro na kasar nan, kan kalubalen da hukumomin tsaron kasar ke ci gaba da fuskanta, wanda irin wadannan kalubalen, an kirkire su ne kawai.

Kazalika, akan kuma samu takardama ko rashin jituwa, a tsakanin wadannan hukumomin tsaron kasar, wanda kamata ya yi a ce, sun hada kansu a waje daya wajen samun bayanai.

Yin amfani da fasahar kimiyyar zamani wajen samun bayanai na sirri, a tsakanin hukumomin tsaron kasar, na daya daga cikin abubuwa masu mahimmanci.

Domin gudanar da aikin, ba tare dayin dabarun samun bayanan sirri ba, tamkar fargar daji ne.

A ra’ayin mu, babu wani dalili da zai sanya a ce, an rasa rayukan ‘yan sandan kasa, a cikin wannan gajeren lokacin.

Muna ganin ya zama wajibi, mahukutan ‘yan sandan kasa, su tabbatar da sun dauki matakan da suka dace, wajen kare rayukan jami’an.

Kazalika, muna son mu kara nanata cewa, aikin ‘yan sandan ba wai aiki ne, na jeka ka kashe kanka ba, kuma bai katama a rinka yiwa aikin kallon haka ba.

Ba da ce, ace aikin ne, na mutuwa domin kare kasa ba, kamata ya yi, aikin ya zamo aiki ne, na kare kasa kuma jami’I ya kasance a raye, domin ya sanar da labarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yansanda
Ra'ayinmu

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Fyade
Ra'ayinmu

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Ra'ayinmu

A Daina Gaggawar Murnar Samun Nasara Kan Ta’addanci A Nijeriya

August 29, 2025
Next Post
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Jami'an Tsaron Nijeriya Sun Hallaka 'Yan Ta'adda 8,034 A 2024 – ONSA

LABARAI MASU NASABA

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi

October 16, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.