• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Kai: Kwamishinan ‘Yansanda Ya Bada Umarnin Yin Bincike Kan Mutuwar Jami’in Dansanda A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kisan Kai: Kwamishinan ‘Yansanda Ya Bada Umarnin Yin Bincike Kan Mutuwar Jami’in Dansanda A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan ‘yansandan Jihar Kebbi, CP Ahmed Magaji-Kontagora, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan al’amuran da suka faru na mutuwar ASP Shu’aibu Sani Mulunfashi.

Hakan na kunshe ne a cikin wata takardar manema labarai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansanda DSP Nafi’u Abubakar kuma aka rabawa manema labarai a Birnin Kebbi.

  • Barazanar Harin Abuja: ‘Yan Ta’adda Ba Sa Bayyana Lokaci Da Wurin Kai Hari – Shehu Sani 
  • Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

Wanda a ranar 19 ga Oktoba, 2022 da misalin karfe 2:10 na rana , wani ASP Abdullahi Garba, jami’in ‘yan sanda na Sauwa, ya samu sabani da ASP Shu’aibu Sani Malunfashi, jami’in sashen binciken aikata laifuka na II, hedikwatar ‘yan sanda ta Argungu, a wajen kamun kifi na garin Argungu. A dalilin haka ne suka yi artabu da juna a gaban shagon ASP Abdullahi Garba.

A yayin da ake fafatawa, ASP Abdullahi Garba ya yi amfani da almakashi ya daba wa ASP Shu’aibu Sani Malunfashi a hakarkarinsa na hagu. Da samun rahoton, jami’in ‘yan sanda na Argungu, sun garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka damke jami’in da ya aikata laifin.

Bisa ga hakan ne aka garzaya da ASP Shu’aibu Sani Malunfashi zuwa Asibitin tunawa da Sarki Yahaya da ke Birnin Kebbi, inda Likita ya tabbatar da mutuwarsa.

Labarai Masu Nasaba

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

Sakamakon haka, jami’in ‘yan sanda da ya aikata laifin, ASP Abdullahi Garba, aka tsare shi a sashin binciken manyan laifuka na jihar da ke Birnin Kebbi, yayin da kuma aka mika binciken nasa zuwa sashin kisan kai domin gudanar da bincike mai zurfi don gano musababbin lamarin.

Kazalika, Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kebbi ya aike da tawagar manyan jami’an ‘yan sanda domin ta’aziyya ga ‘yan uwa da abokan arziki wanda ya rasu tare da addu’ar Allah ya jikan Asp Shu’aibu Sani Malunfashi ya gafarta masa.

Bugu da Kari CP Ahmed Magaji Kontagora ya kuma yi Allah-wadai da matakin da jami’in da ya yi kuskure ya nuna wanda ya saba wa koyarwar ‘yan sanda da dokar ‘yan sanda da kuma sauran dokokin da suka shafi kundin kasar Nijeriya.

Hakazalika, CP ya gargadi jami’an rundunar da su zauna lafiya a kodayaushe tare da kai rahoton korafe-korafen su ga sassan da suka dace a cikin rundunar domin gyara a maimakon daukar doka ga hannu.

Daga karshe kwamishinan ya tabbatar wa da jama’a cewa, za a yi adalci wajen gudanar da bincike kan lamarin sannan kuma za a bayyana sakamakon binciken.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASPBincikeKebbiKisaKwamishinan 'Yansanda
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabar Tanzania Za Ta Zama Shugabar Afirka Ta Farko Da Za Ta Ziyarci Sin Bayan Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

Next Post

Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

Related

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
Manyan Labarai

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

2 hours ago
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Manyan Labarai

DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci

9 hours ago
Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki

1 day ago
Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
Manyan Labarai

Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi

1 day ago
nijeriya
Manyan Labarai

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

2 days ago
Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu

2 days ago
Next Post
Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

LABARAI MASU NASABA

Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

June 14, 2025
Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba

June 14, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya

June 14, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

June 14, 2025
Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe

June 14, 2025
Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u

June 14, 2025
An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka

June 14, 2025
Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata

June 14, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

June 14, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi

June 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.