• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Kai: Kwamishinan ‘Yansanda Ya Bada Umarnin Yin Bincike Kan Mutuwar Jami’in Dansanda A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kisan Kai: Kwamishinan ‘Yansanda Ya Bada Umarnin Yin Bincike Kan Mutuwar Jami’in Dansanda A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan ‘yansandan Jihar Kebbi, CP Ahmed Magaji-Kontagora, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan al’amuran da suka faru na mutuwar ASP Shu’aibu Sani Mulunfashi.

Hakan na kunshe ne a cikin wata takardar manema labarai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansanda DSP Nafi’u Abubakar kuma aka rabawa manema labarai a Birnin Kebbi.

  • Barazanar Harin Abuja: ‘Yan Ta’adda Ba Sa Bayyana Lokaci Da Wurin Kai Hari – Shehu Sani 
  • Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

Wanda a ranar 19 ga Oktoba, 2022 da misalin karfe 2:10 na rana , wani ASP Abdullahi Garba, jami’in ‘yan sanda na Sauwa, ya samu sabani da ASP Shu’aibu Sani Malunfashi, jami’in sashen binciken aikata laifuka na II, hedikwatar ‘yan sanda ta Argungu, a wajen kamun kifi na garin Argungu. A dalilin haka ne suka yi artabu da juna a gaban shagon ASP Abdullahi Garba.

A yayin da ake fafatawa, ASP Abdullahi Garba ya yi amfani da almakashi ya daba wa ASP Shu’aibu Sani Malunfashi a hakarkarinsa na hagu. Da samun rahoton, jami’in ‘yan sanda na Argungu, sun garzaya wurin da lamarin ya faru, inda suka damke jami’in da ya aikata laifin.

Bisa ga hakan ne aka garzaya da ASP Shu’aibu Sani Malunfashi zuwa Asibitin tunawa da Sarki Yahaya da ke Birnin Kebbi, inda Likita ya tabbatar da mutuwarsa.

Labarai Masu Nasaba

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sakamakon haka, jami’in ‘yan sanda da ya aikata laifin, ASP Abdullahi Garba, aka tsare shi a sashin binciken manyan laifuka na jihar da ke Birnin Kebbi, yayin da kuma aka mika binciken nasa zuwa sashin kisan kai domin gudanar da bincike mai zurfi don gano musababbin lamarin.

Kazalika, Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kebbi ya aike da tawagar manyan jami’an ‘yan sanda domin ta’aziyya ga ‘yan uwa da abokan arziki wanda ya rasu tare da addu’ar Allah ya jikan Asp Shu’aibu Sani Malunfashi ya gafarta masa.

Bugu da Kari CP Ahmed Magaji Kontagora ya kuma yi Allah-wadai da matakin da jami’in da ya yi kuskure ya nuna wanda ya saba wa koyarwar ‘yan sanda da dokar ‘yan sanda da kuma sauran dokokin da suka shafi kundin kasar Nijeriya.

Hakazalika, CP ya gargadi jami’an rundunar da su zauna lafiya a kodayaushe tare da kai rahoton korafe-korafen su ga sassan da suka dace a cikin rundunar domin gyara a maimakon daukar doka ga hannu.

Daga karshe kwamishinan ya tabbatar wa da jama’a cewa, za a yi adalci wajen gudanar da bincike kan lamarin sannan kuma za a bayyana sakamakon binciken.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASPBincikeKebbiKisaKwamishinan 'Yansanda
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabar Tanzania Za Ta Zama Shugabar Afirka Ta Farko Da Za Ta Ziyarci Sin Bayan Babban Taron Wakilan JKS Karo Na 20

Next Post

Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

Related

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

8 hours ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

11 hours ago
Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka
Manyan Labarai

Mafi Ƙarancin Albashin ₦70,000 Ba Zai Iya Tsamo ‘Yan Nijeriya Daga Ƙangin Talauci Ba – Amurka

17 hours ago
Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 
Manyan Labarai

Sarkin Musulmi Ya Taya Ladoja Murnar Zama Sabon Sarkin Ƙasar Ibadan 

22 hours ago
Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 
Manyan Labarai

Safarar Yara: Gwamnatin Adamawa Ta Haɗa Yara 14 Da Iyayensu Da Aka Ceto A Anambra 

2 days ago
Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50
Manyan Labarai

Hare-hare: Adadin Mutanen Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Katsina Ya Haura 50

2 days ago
Next Post
Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

Jarin Ketare Da Aka Zuba Kai Tsaye A Kasar Sin Ya Haura Yuan Triliyan 1 Daga Janairu Zuwa Satumba

LABARAI MASU NASABA

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

August 21, 2025
Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Sin Ya Karu Da Kashi 3.5% A Watanni Bakwai Na Farkon Bana

August 21, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Na “Sautin Zaman Lafiya” A Washington

August 21, 2025
Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

August 21, 2025
Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

Amfani Da Wutar Lantarki A Sin Ya Habaka Sosai A Watan Yuli

August 21, 2025
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

August 21, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Jihar Xizang Mai Cin Gashin Kanta

August 21, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Gwaji Na Samun Lamunin Waje Ga Bangaren Makamashi Mai Tsafta

August 21, 2025
NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

NGF Ta Yi Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifin Gwamna Ododo

August 21, 2025
Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

Kura Za Ta Ce Da Kare Maye

August 21, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.