• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya, Ra'ayoyi
0
Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunkuri na ceto kananan hukumomi daga dabaibayin gwamnoni, gwamnatin tarayya ta maka daukacin gwamnonin kasar nan 36 a gaban kotun koli na neman a sakar wa kananan hukumomi mara su ci gashin kansu.

Karamar hukuma ita ce gwamnati mafi kusa da jama’a, kuma ita ke bunkasa al’umma a matakin farko. Sai dai kuma, ingantaccen shugabanci a kananan hukumomi ya gamu da cikas sakamakon irin dabaibayin da gwamnonin jihohi ke musu.

  • Karin Albashi Ya Zama Karfen Kafa A Nijeriya
  • Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Naira 62,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi 

Kudaden kananan hukumomi a asusun tarayya da ake biya duk wata suna zuwa ne daga gwamnatocin jihohinsu.

A cikin karar mai lamba SC/CB/343/2024, da babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a, Prince Lateef Fagbemi, ya shigar, gwamnatin tarayya tana neman a bai wa kananan hukumomi cikkiyar ‘yan ci a kasan a matsinsu na mataki na uku na gwamnati.

Ta kuma bukaci kotun kolin da ta bayar da umarni tare da haramta wa gwamnonin jihohi rusa shugabannin kananan hukumomin da aka zaba ba da kuma bayar da umarnin bayan kudaden kananan hukumomi kai tsaye ga asusunsu daidai da yadda kundin tsarin mulki ya tanada ba a asusun hadin gwiwa ba da gwamnoni suka kirkira ba bisa ka’ida ba.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

A karar da gwamnatin tarayya ta shigar, gwamnatin tarayya na bukatar kotun koli ta bayar da umarni na dakatar da gwamnonin ci gaba da kafa kwamitocin rikon kwarya da za su tafiyar da al’amuran kananan hukumomi wanda ya saba wa tsarin mulkin dimokuradiyya da aka amince da shi.

Haka kuma gwamnatin tarayya ta yi ikirarin cewa Nijeriya a matsayinta ta tarayya, ita ce ta kirkiro kundin tsarin mulki na 1999, wadda aka yi wa kwaskwarima, inda shugaban kasa, a matsayinsa na shugaban gwamnatin tarayya, ya rantse da cewa zai tabbatar da bin tsarin kundin mulki.

Tun bayan zuwan mulkin dimokuradiyya a kasar nan a shekarar 1999, gwamnatocin jihohi ke dabaibaye kananan hukumomi 774 da ke kasar nan.

Ba wai kawai gwamnoni na zabar makusantansu da za su gudanar da harkokin kananan hukumomi ba, har ma suna zayyana yadda za a kashe kudadensu, musamman kason da ake samu daga asusun tarayya.

Wannan lamari yana gunana ne a tsakanin jam’iyyun siyasa masu mulkin gwamnatocin jihohi karkashin kwamishinonin kananan hukumomi da al’amuran sarauta.

Wannan lamari ya sa kananan hukumomi sun rasa ‘yancin kai na gudanar da harkokin kudade da kuma ‘yancin gudanar da ayyuka, wanda ya mayar da su baya da kuma kasa samar da muhimman ayyukan da al’umm za su amfana.

Duk wani yunkuri na bai wa kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kai ta hanyar gyaran kundin tsarin mulkin kasa, gwamnonin sun toshe.

Hatta kotuna da dama, ciki har da kotun koli, sun yi kokarin shiga tsakani a lokuta da dama kan yadda gwamnonin ke nuna halin ko-in-kula da kananan hukumomi ke yi ba tare da cimma wata nasara ba.

Ba wai kawai ba a gudanar da zabuka ba ne ko kuma ana yawan cire shugabanni kananan hukumomi da kansiloli kadai, ana yawan kafa kwamitocin riko domin gudanar da harkokin kananan hukumomi duk saboda kudaden shiga da suke samu.

A yayin da ake ci gaba da sauraren karar a makon da ya gabata, kwamitin alkalai guda bakwai na kotun kolin karkashin jagorancin mai shari’a Garba Lawal, ya umarci gwamnonin wanda babban lauyoyin jihohi suka wakilta da su gabatar da takardar kariyarsu ga wannan sammacin cikin kwanaki bakwai. An dai dage sauraron karar zuwa ranar 13 ga watan Yunin 2024.

Abin jira a gani dai shi ne, yadda gwamnatin tarayya za ta bi sawun karar a lokacin da kotun koli za ta yanke hukunci ko dai ta samu nasara ko akashin haka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DemocracyDimokuraɗiyyaLocal governmentPolitics
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumonin Saudiya Sun Tsananta Fatattakar Bakin Haure

Next Post

Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

LABARAI MASU NASABA

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.