• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Ceto Kananan Hukumomi Daga Gwamnoni?

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Gwamnati

A wani yunkuri na ceto kananan hukumomi daga dabaibayin gwamnoni, gwamnatin tarayya ta maka daukacin gwamnonin kasar nan 36 a gaban kotun koli na neman a sakar wa kananan hukumomi mara su ci gashin kansu.

Karamar hukuma ita ce gwamnati mafi kusa da jama’a, kuma ita ke bunkasa al’umma a matakin farko. Sai dai kuma, ingantaccen shugabanci a kananan hukumomi ya gamu da cikas sakamakon irin dabaibayin da gwamnonin jihohi ke musu.

  • Karin Albashi Ya Zama Karfen Kafa A Nijeriya
  • Da Dumi-Dumi: Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Naira 62,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi 

Kudaden kananan hukumomi a asusun tarayya da ake biya duk wata suna zuwa ne daga gwamnatocin jihohinsu.

A cikin karar mai lamba SC/CB/343/2024, da babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a, Prince Lateef Fagbemi, ya shigar, gwamnatin tarayya tana neman a bai wa kananan hukumomi cikkiyar ‘yan ci a kasan a matsinsu na mataki na uku na gwamnati.

Ta kuma bukaci kotun kolin da ta bayar da umarni tare da haramta wa gwamnonin jihohi rusa shugabannin kananan hukumomin da aka zaba ba da kuma bayar da umarnin bayan kudaden kananan hukumomi kai tsaye ga asusunsu daidai da yadda kundin tsarin mulki ya tanada ba a asusun hadin gwiwa ba da gwamnoni suka kirkira ba bisa ka’ida ba.

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

A karar da gwamnatin tarayya ta shigar, gwamnatin tarayya na bukatar kotun koli ta bayar da umarni na dakatar da gwamnonin ci gaba da kafa kwamitocin rikon kwarya da za su tafiyar da al’amuran kananan hukumomi wanda ya saba wa tsarin mulkin dimokuradiyya da aka amince da shi.

Haka kuma gwamnatin tarayya ta yi ikirarin cewa Nijeriya a matsayinta ta tarayya, ita ce ta kirkiro kundin tsarin mulki na 1999, wadda aka yi wa kwaskwarima, inda shugaban kasa, a matsayinsa na shugaban gwamnatin tarayya, ya rantse da cewa zai tabbatar da bin tsarin kundin mulki.

Tun bayan zuwan mulkin dimokuradiyya a kasar nan a shekarar 1999, gwamnatocin jihohi ke dabaibaye kananan hukumomi 774 da ke kasar nan.

Ba wai kawai gwamnoni na zabar makusantansu da za su gudanar da harkokin kananan hukumomi ba, har ma suna zayyana yadda za a kashe kudadensu, musamman kason da ake samu daga asusun tarayya.

Wannan lamari yana gunana ne a tsakanin jam’iyyun siyasa masu mulkin gwamnatocin jihohi karkashin kwamishinonin kananan hukumomi da al’amuran sarauta.

Wannan lamari ya sa kananan hukumomi sun rasa ‘yancin kai na gudanar da harkokin kudade da kuma ‘yancin gudanar da ayyuka, wanda ya mayar da su baya da kuma kasa samar da muhimman ayyukan da al’umm za su amfana.

Duk wani yunkuri na bai wa kananan hukumomi ‘yancin cin gashin kai ta hanyar gyaran kundin tsarin mulkin kasa, gwamnonin sun toshe.

Hatta kotuna da dama, ciki har da kotun koli, sun yi kokarin shiga tsakani a lokuta da dama kan yadda gwamnonin ke nuna halin ko-in-kula da kananan hukumomi ke yi ba tare da cimma wata nasara ba.

Ba wai kawai ba a gudanar da zabuka ba ne ko kuma ana yawan cire shugabanni kananan hukumomi da kansiloli kadai, ana yawan kafa kwamitocin riko domin gudanar da harkokin kananan hukumomi duk saboda kudaden shiga da suke samu.

A yayin da ake ci gaba da sauraren karar a makon da ya gabata, kwamitin alkalai guda bakwai na kotun kolin karkashin jagorancin mai shari’a Garba Lawal, ya umarci gwamnonin wanda babban lauyoyin jihohi suka wakilta da su gabatar da takardar kariyarsu ga wannan sammacin cikin kwanaki bakwai. An dai dage sauraron karar zuwa ranar 13 ga watan Yunin 2024.

Abin jira a gani dai shi ne, yadda gwamnatin tarayya za ta bi sawun karar a lokacin da kotun koli za ta yanke hukunci ko dai ta samu nasara ko akashin haka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

Rikicin Sarautar Kano: Kallo Ya Sake Komawa Kotu

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025
An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.