• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kun San Labarin Wutar Dajin Da Ta Jefa Aljeriya Cikin Mawuyacin Hali?

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Ko Kun San Labarin Wutar Dajin Da Ta Jefa Aljeriya Cikin Mawuyacin Hali?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Korayen tsaunukan yankin Tizi Ouzou na Aljeriya, masu lullube da lambun zaitun da bishoyi masu cikar ganye, yanzu wutar daji sama da dari ta lalata su cikin mako biyu.

Ana iya jin zafin wutar daga wuri mai nisan gaske.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti
  • Waiwaye Game Da Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida Ta Duniya

A wani gidan sayar da mai a lardin Bouira, wani mutum mai zuba wa ababen hawa man fetir ya wahala da yanayi ya sauya ya koma na tsananin zafi.

“Zafin na fitowa ne daga tsaunukan. Ban taba ganin wutar daji irin wannan ba,” ya shaida mana.

Wutar daji ba sabon abu ba ne a Aljeriya, musamman a yankin Arewa maso gabashi na Tizi Ouzou.

Labarai Masu Nasaba

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

A iya cewa ma abu ne da aka saba gani akai-akai da masu aikin agaji ke fama duk shekara.

Kuma wutar dajin na yin darna mai dumbin yawa duba da rashin ruwan sama da iska mai karfin gaske da ke kadawa.

Dubban kadada a kusa da kauyukan Larbaâ Nath Irathen, Beni Douala da Aït Mesbah ne wutar ta mamaye ta kona bishoyoyin masu yawan ganye da a baya suke jere a kan tsaunukan.

Rahotannin farko-farko sun gano cewa wutar ta wannan shekarar ta yi barna ga dazukan Algeriya fiye da duka watar dajin da aka yi daga shekarun 2008 zuwa 2020 gaba daya.

Akalla mutum 90 sun mutu yayin kashe wutar ciki har da sojoji 33 da aka bai wa lambar yabo.

Duk da kokarin kashe wutar daji duk shekarar, da kuma ikirarin kasafin kudi na sojoji mafi yawa a Afrika, Aljeriya ba ta da jiragen sama na kashe wutar daji.

A maimakon haka, wasu ‘yan kananan jirage ne kirar Mi-26 da ke iya daukar bokiti mai girman lita 1,000 suka yi kokarin kashe wutar.

Don haka, dole gwamnati ta nemi agaji daga Tarayyar Turai kuma ran 12 ga Agusta, Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya aika masu da jirage biyu.

Mutanen kauyen Beni Douala sun shiga aikin kashe wutar da tebir da rassan bishiya da duk wani abu da suke da shi.

“Kila fasfo din sa ne ya lalace,” Fethi Fellah wani dan agaji ya fada cikin raha lokacin da aka tambaye shi ko ya ga jirgi kashe wuta.

“Baya ga ‘yan kwana-kwana, babu wand aya fito ya agaza mana,” ya ce a lokacin da yake karkatar da jerin motoci daga tsaunukan zuwa birnin Tizi Ouzou inda iyalai suka taru a wasu rumfunan agaji.

Daya daga cikin wuraren shi ne babban dakin taron Le Printemps da ke karbbar mutanen da suka tsere daga muhallansu.

Fuskokinsu sun cika da jajircewa da bacin rai a lokacin da suka fahimci su za su yi wa kansu komai.

“Hukumomi ba su agaza mana wajen tserewa ba, dole muka dogara da masu aikin sa kai da ke zuwa daga kauye zuwa kauye,” a cewar Ines, wata ma’aikaciyar sa kai.

“Hukumomin na da wani bangare na alhakin yawan mutanen da suka mutu. Duk shekarar muna samun wutar daji kuma har yanzu ba a dauki wasu matakai ba,” a cewarta.

Daga Firai Minista Aymen Benabderrahmane da Shugaba Abdelmadjid Tebboune sun ce wasu bata gari ne ke sa wutar dajin, sai dai kuma ba su ba da wata kwakkwarar hujja kan haka ba.

Sun zarfi kungiyoyin ‘yan aware a yankin kabyle a kusa da Tizi Ouzou kuma sun ce za su sake duba alakar diflomasiyya da Maroko wadda ta ke zargi da goyon bayan kungiyoyin.

Sai dai sun manta da cewa kasashen da ke kusa da yankin Mediterranean suna fama da wutar daji a makonnin baya-bayan nan ciki har da Turkiyya da Girka da Cyprus da Italiya da Faransa.

Mai yiwuwa sauyin yanayi a yankin da taka rawa wajen faruwar abubuwan da ke janyo wutar dajin.

Sai dai har yanzu dumamar yanayi ba ya cikin wani batu da ake tattaunawa a Ajeriya.

Kuma asarar rai da ta muhalli da ake samu sanadiyyar bala’o’i sun fara yawan da ba za a iya kawar da kai ba.

Wutar daji ba ita ce kawai alamar sauyin yanayi a Aljeriya ba.

Hamadar Sahara, wadda ita ce kashi 80 cikin 100 na kasar na kara girma.

Ta karu da kashi 10 cikin dari a shekaru 100 da suka gabata a cewar mujallar Journal of Climate.

Karuwar hamadar na toshe hanyoyin da makiyaya ke bi don sama wa dabbobi abinci kuma tana tursasa wa manoma kara hakar kasa don samun ruwa.

Ga al’ummun da dama can suke daga gefe-gefen hamadar, dumamar yanayi na kara jefa su cikin mawuyacin hali musamman a lokacin bazara.

Dalibai a lardin Adrar, misali, na cikin rukunin dalibai da ke baya-baya a kokarin makaranta a kasar, saboda ba a gina azuzuwansu don iya zama a lokacin tsananin zafin yankin ba.

A Algiers babban birnin kasar, rashin isasshen ruwa ya sa wasu sassan birnin ba sa samun ruwa a famfo sai na dan wani lokaci a wuni guda.

Shugaba Tebboune ya sanar da cewa za a samar da tashoshin cire gishiri daga ruwan teku guda uku don shawo kan matsalar.

Sai dai, idan ba a dauki sauyin yanayi da muhimmanci ba, sannan a sa manufofi kan muhalli, irin wadannan ayyukan za su samar da sauki ne kawai a gajeren zango.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Wutar Daji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Thomas: Daya Daga Cikin Wutar Daji Mafi Muni A Tarihin California Ta Amurka

Next Post

Maimaici: Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Related

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

4 hours ago
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa
Ilimi

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

5 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

6 hours ago
Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS
Labarai

Yunwa Da Talauci Ne Ke Barazana Ga Harkar Tsaro A Kasar Nan — NSA, CDS

9 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

11 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

11 hours ago
Next Post
Maimaici: Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Maimaici: Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don ÆŠaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.