• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kun San Labarin Wutar Dajin Da Ta Jefa Aljeriya Cikin Mawuyacin Hali?

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Ko Kun San Labarin Wutar Dajin Da Ta Jefa Aljeriya Cikin Mawuyacin Hali?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Korayen tsaunukan yankin Tizi Ouzou na Aljeriya, masu lullube da lambun zaitun da bishoyi masu cikar ganye, yanzu wutar daji sama da dari ta lalata su cikin mako biyu.

Ana iya jin zafin wutar daga wuri mai nisan gaske.

  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Soke Nasarar Zababben Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti
  • Waiwaye Game Da Ranar ‘Yancin ‘Yan Jarida Ta Duniya

A wani gidan sayar da mai a lardin Bouira, wani mutum mai zuba wa ababen hawa man fetir ya wahala da yanayi ya sauya ya koma na tsananin zafi.

“Zafin na fitowa ne daga tsaunukan. Ban taba ganin wutar daji irin wannan ba,” ya shaida mana.

Wutar daji ba sabon abu ba ne a Aljeriya, musamman a yankin Arewa maso gabashi na Tizi Ouzou.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

A iya cewa ma abu ne da aka saba gani akai-akai da masu aikin agaji ke fama duk shekara.

Kuma wutar dajin na yin darna mai dumbin yawa duba da rashin ruwan sama da iska mai karfin gaske da ke kadawa.

Dubban kadada a kusa da kauyukan Larbaâ Nath Irathen, Beni Douala da Aït Mesbah ne wutar ta mamaye ta kona bishoyoyin masu yawan ganye da a baya suke jere a kan tsaunukan.

Rahotannin farko-farko sun gano cewa wutar ta wannan shekarar ta yi barna ga dazukan Algeriya fiye da duka watar dajin da aka yi daga shekarun 2008 zuwa 2020 gaba daya.

Akalla mutum 90 sun mutu yayin kashe wutar ciki har da sojoji 33 da aka bai wa lambar yabo.

Duk da kokarin kashe wutar daji duk shekarar, da kuma ikirarin kasafin kudi na sojoji mafi yawa a Afrika, Aljeriya ba ta da jiragen sama na kashe wutar daji.

A maimakon haka, wasu ‘yan kananan jirage ne kirar Mi-26 da ke iya daukar bokiti mai girman lita 1,000 suka yi kokarin kashe wutar.

Don haka, dole gwamnati ta nemi agaji daga Tarayyar Turai kuma ran 12 ga Agusta, Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya aika masu da jirage biyu.

Mutanen kauyen Beni Douala sun shiga aikin kashe wutar da tebir da rassan bishiya da duk wani abu da suke da shi.

“Kila fasfo din sa ne ya lalace,” Fethi Fellah wani dan agaji ya fada cikin raha lokacin da aka tambaye shi ko ya ga jirgi kashe wuta.

“Baya ga ‘yan kwana-kwana, babu wand aya fito ya agaza mana,” ya ce a lokacin da yake karkatar da jerin motoci daga tsaunukan zuwa birnin Tizi Ouzou inda iyalai suka taru a wasu rumfunan agaji.

Daya daga cikin wuraren shi ne babban dakin taron Le Printemps da ke karbbar mutanen da suka tsere daga muhallansu.

Fuskokinsu sun cika da jajircewa da bacin rai a lokacin da suka fahimci su za su yi wa kansu komai.

“Hukumomi ba su agaza mana wajen tserewa ba, dole muka dogara da masu aikin sa kai da ke zuwa daga kauye zuwa kauye,” a cewar Ines, wata ma’aikaciyar sa kai.

“Hukumomin na da wani bangare na alhakin yawan mutanen da suka mutu. Duk shekarar muna samun wutar daji kuma har yanzu ba a dauki wasu matakai ba,” a cewarta.

Daga Firai Minista Aymen Benabderrahmane da Shugaba Abdelmadjid Tebboune sun ce wasu bata gari ne ke sa wutar dajin, sai dai kuma ba su ba da wata kwakkwarar hujja kan haka ba.

Sun zarfi kungiyoyin ‘yan aware a yankin kabyle a kusa da Tizi Ouzou kuma sun ce za su sake duba alakar diflomasiyya da Maroko wadda ta ke zargi da goyon bayan kungiyoyin.

Sai dai sun manta da cewa kasashen da ke kusa da yankin Mediterranean suna fama da wutar daji a makonnin baya-bayan nan ciki har da Turkiyya da Girka da Cyprus da Italiya da Faransa.

Mai yiwuwa sauyin yanayi a yankin da taka rawa wajen faruwar abubuwan da ke janyo wutar dajin.

Sai dai har yanzu dumamar yanayi ba ya cikin wani batu da ake tattaunawa a Ajeriya.

Kuma asarar rai da ta muhalli da ake samu sanadiyyar bala’o’i sun fara yawan da ba za a iya kawar da kai ba.

Wutar daji ba ita ce kawai alamar sauyin yanayi a Aljeriya ba.

Hamadar Sahara, wadda ita ce kashi 80 cikin 100 na kasar na kara girma.

Ta karu da kashi 10 cikin dari a shekaru 100 da suka gabata a cewar mujallar Journal of Climate.

Karuwar hamadar na toshe hanyoyin da makiyaya ke bi don sama wa dabbobi abinci kuma tana tursasa wa manoma kara hakar kasa don samun ruwa.

Ga al’ummun da dama can suke daga gefe-gefen hamadar, dumamar yanayi na kara jefa su cikin mawuyacin hali musamman a lokacin bazara.

Dalibai a lardin Adrar, misali, na cikin rukunin dalibai da ke baya-baya a kokarin makaranta a kasar, saboda ba a gina azuzuwansu don iya zama a lokacin tsananin zafin yankin ba.

A Algiers babban birnin kasar, rashin isasshen ruwa ya sa wasu sassan birnin ba sa samun ruwa a famfo sai na dan wani lokaci a wuni guda.

Shugaba Tebboune ya sanar da cewa za a samar da tashoshin cire gishiri daga ruwan teku guda uku don shawo kan matsalar.

Sai dai, idan ba a dauki sauyin yanayi da muhimmanci ba, sannan a sa manufofi kan muhalli, irin wadannan ayyukan za su samar da sauki ne kawai a gajeren zango.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Wutar Daji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Thomas: Daya Daga Cikin Wutar Daji Mafi Muni A Tarihin California Ta Amurka

Next Post

Maimaici: Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

6 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

8 hours ago
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno
Labarai

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

10 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

13 hours ago
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu
Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

15 hours ago
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato
Labarai

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

16 hours ago
Next Post
Maimaici: Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

Maimaici: Wasu Daga Cikin Manhajojin Da Ke Bata Wayar Android

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.