Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Ko Ma’aikacin INEC Ba Zai Iya Murde Zaben Ekiti Ba –Yakubu

by
4 years ago
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Yayin da Shugaban Jam’iyyar PDP da gwamnan jihar Ekiti, Ayo Fayose, su ka koka da zargin yunkurin tafka magudi a zaben gwamnan jihar Ekiti, INEC ta ce zargin ba abin kamawa ba ne kuma ba gaskiya ba ne, domin ko da jami’in hukumar bai isa ya iya aikata magudi a zaben ba, saboda tsari da kuma matakan tsaron da a ka saka a zaben.
Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya fito karara ya mayar da martanin ya na mai cewa, babu wani ma’aikacin hukumarsa da zai iya yin magudi ko murde zaben gwamnan jihar Ekiti, kamar yadda wasu ke zargi. Mahmood Yakubu ya bayyana haka a cikin makon nan, yayin da ya ke ganawa da jam’iyyun siyasa a Cibiyar Zabe ta INEC a Abuja.
“Ina tabbatar mu ku da cewa tsarin zaben da mu ka shigo da shi ya wuce tunanin wani ko ma wane ne ya yi magudi ko ya murde sakamakon,” in ji shi.
Yakubu ya ce an dauki tsauraren matakan da zai iya cewa idan dai wani zai iya murde zaben, to rakumi zai iya shiga ta kofar allura ya fita.
“Zargin da wasu ke yi wai an kwafi katin rajista da kuma na’urar karanta katin kada kuri’a, wannan duk shaci-fadi ne kawai.”
Tun da farko a jawabin nasa, Yakubu ya fara ne da shaida wa shugabannin jam’iyyun da ya gana da su irin shirin da INEC ta yi na gudanar da zabukan cike gurbi a jihohin Bauchi, Katsina, Taraba da wasu wurare.
Daga nan sai ya gangara kan zaben gwamnan jihar Ekiti, da ya ce za a gudanar a rumfunan zabe 2,195 da ke cikin mazabu 177 a fadin jihar.
Ya ce dukkan fadin kananan hukumomin jihar 17 za a gudanar da zaben, wanda ya ce jam’iyyun siyasa 35 su ka za su shiga zaben.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Mutanen Alkaleri Sun Yaba Da Ingancin Aikin Hanyar Bauchi Zuwa Gombe

Next Post

Kungiyar Red Card Ta Yi Taron Wayar Da Masu Zabe A Bauchi

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
3 hours ago
0

...

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan  Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

Yadda Jirgin Kasa Ya Halaka Daruruwan Dabbobi A Hanyar Kaduna Zuwa Abuja

by Sulaiman Idris
5 hours ago
0

...

Cafke Wadanda Ake Zargi Da Kisan Deborah: Zanga-zanga Ta Barke A Sokoto

Kisa Kan Zargin Batanci Ga Annabi: An Tsare Wadanda Aka Kama A Gidan Gyara Hali

by
5 hours ago
0

...

An Yi Lugudan Wuta Ta Jiragen Yaki Kan Isis An Kashe Kwamandanta Bin-umar A Tabkin Chadi

Dakarun MNJTF Sun Yi Barin Wuta Kan ‘Yan Boko Haram Sun Kashe 300 A Tafkin Chadi

by Leadership Hausa
6 hours ago
0

...

Next Post
Kungiyar Red Card Ta Yi Taron Wayar Da Masu Zabe A Bauchi

Kungiyar Red Card Ta Yi Taron Wayar Da Masu Zabe A Bauchi

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: