• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala

by Abubakar Sulaiman
7 months ago
in Nishadi
0
Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da wasu ke daukar harkar fim a matsayin wata hanya na neman kudi kawai, daya daga cikin manyan dattijai a cikin masana’antar Kannywood Alhaji Dan Asabe Garba ko kuma Olala ya ce akwai wasu ayyuka da ba zai iya yi ba ko nawa kuwa za a ba shi.

A lokacin da zan shiga harkar fim, masoya,iyalai da ‘yan uwa sun so su hana ni saboda a nasu tunanin zan iya yin wani abinda zai iya zubar masu da mutuncinsu amma ganin ina matukar sha’awar harkar ya sa dole suka hakura na shiga amma da sharudda biyu, na farko shi ne ba zan taba fitowa a cikin shirin fim a matsayin Dan Daudu ba hakazalika ba zan fito a matsayin Kwarto ba.

  • Na Samu Wata Harkar Da Ta Fi Sana’ar Fim Kawo Kudade -Ali Dawayya
  • Ana Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Malamai A Zamanin Baya -Ali Rabi’u Ali

Yanzu haka a kan wannan matsaya ya sa suka barni ina yin wannan harkar, saboda haka ko nawa wani zai bani a kan in karya wannan alkawari da na daukar wa ‘yan uwana da iyalina ba zan karba ba saboda mutunci ya fi komai in ji Dan Asabe Olala wanda ya shafe tsawon shekaru ana damawa da shi a masana’antar Kannywood.

Dangane da kalubalen da masana’antar Kannywood ke fuskanta a halin yanzu, Olala ya ce daga cikin kalubale da ke damun Kannywood akwai rashin jari wanda ya sa an samu karancin yin fina-finai ba kamar a kwanakin  baya da za kaga ayyuka sun yi yawa ba,a wancan lokacin a kan hada karfi mutum biyu ko uku su shirya fim daya saboda za a kai fim kasuwa a sayar kowa a bashi kudinsa.

Amma yanzu saboda yadda aka koma fina-finai masu dogon zango da dama mutane basu da isassun kudaden da za su saka wajen shirya manyan fina-finai da ake shiryawa a yanzu, saboda haka da ace zan samu shugabancin wannan masana’antar zan mayar da hankalina kacokan wajen hada kan mambobin masana’antar ta Kannywood.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Sannan kuma in tafi wajen samo masu hannu da shuni domin su zo su zuba hannayen jarinsu a wannan masana’antar, zaka ga da dama mutane na sha’war zuba hannayen jarinsu a wannan masana’antar amma ba su san yadda za su yi ba ko kuma hanyoyin da za su bi wajen ganin ba su yi asarar kudadensu da su ka zuba a harkar ba.

Daga karshe Alhaji Dan Asabe ya shawarci matasa mata da maza da ke da sha’awar shigowa wannan masana’antar domin su fara harkar fim a kan duk wanda zai shigo ya tabbatar da cewar zai iya hakuri har zuwa lokacin da Allah zai nufi ya samu daukaka, domin kuwa a dare daya ba zai samu abin da yake so ba dole sai ya jajirce ya kuma yi hakuri kamar yadda wadanda yake gani sun samu daukaka suka yi kafin shima ya zama wani abu a Kannywood.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FimHausaHausa Fim
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Faransa Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Bisa Matsayin Koli Karo Na 26 

Next Post

Yadda Wasan Manchester Derby Ya Kaya A Etihad 

Related

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa
Nishadi

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

2 weeks ago
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau
Nishadi

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

3 weeks ago
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

3 weeks ago
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda
Nishadi

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

4 weeks ago
Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)
Nishadi

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

1 month ago
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba
Nishadi

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

2 months ago
Next Post
Yadda Wasan Manchester Derby Ya Kaya A Etihad 

Yadda Wasan Manchester Derby Ya Kaya A Etihad 

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Fitowa

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

Sin Ta Gudanar Da Gasar Kirkire-kirkire Ta Daliban Kasa Da Kasa A Yankin Afirka Karo Na Farko

July 26, 2025
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

July 26, 2025
Kwanciyar Aure

Yadda Hadarin Mutuwa Ke Karuwa Yayin Ko Bayan Saduwa Da Iyali

July 26, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Ta Yi Kira Da A Ci Gaba Da Himmatuwa Wajen Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

July 26, 2025
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.