• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala

by Abubakar Sulaiman
9 months ago
in Nishadi
0
Ko Nawa Za A Bani Ba Zan Iya Fitowa A Matsayin Kwarto Ko Dan Daudu A Fim Ba -Dan Asabe Olala
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da wasu ke daukar harkar fim a matsayin wata hanya na neman kudi kawai, daya daga cikin manyan dattijai a cikin masana’antar Kannywood Alhaji Dan Asabe Garba ko kuma Olala ya ce akwai wasu ayyuka da ba zai iya yi ba ko nawa kuwa za a ba shi.

A lokacin da zan shiga harkar fim, masoya,iyalai da ‘yan uwa sun so su hana ni saboda a nasu tunanin zan iya yin wani abinda zai iya zubar masu da mutuncinsu amma ganin ina matukar sha’awar harkar ya sa dole suka hakura na shiga amma da sharudda biyu, na farko shi ne ba zan taba fitowa a cikin shirin fim a matsayin Dan Daudu ba hakazalika ba zan fito a matsayin Kwarto ba.

  • Na Samu Wata Harkar Da Ta Fi Sana’ar Fim Kawo Kudade -Ali Dawayya
  • Ana Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Malamai A Zamanin Baya -Ali Rabi’u Ali

Yanzu haka a kan wannan matsaya ya sa suka barni ina yin wannan harkar, saboda haka ko nawa wani zai bani a kan in karya wannan alkawari da na daukar wa ‘yan uwana da iyalina ba zan karba ba saboda mutunci ya fi komai in ji Dan Asabe Olala wanda ya shafe tsawon shekaru ana damawa da shi a masana’antar Kannywood.

Dangane da kalubalen da masana’antar Kannywood ke fuskanta a halin yanzu, Olala ya ce daga cikin kalubale da ke damun Kannywood akwai rashin jari wanda ya sa an samu karancin yin fina-finai ba kamar a kwanakin  baya da za kaga ayyuka sun yi yawa ba,a wancan lokacin a kan hada karfi mutum biyu ko uku su shirya fim daya saboda za a kai fim kasuwa a sayar kowa a bashi kudinsa.

Amma yanzu saboda yadda aka koma fina-finai masu dogon zango da dama mutane basu da isassun kudaden da za su saka wajen shirya manyan fina-finai da ake shiryawa a yanzu, saboda haka da ace zan samu shugabancin wannan masana’antar zan mayar da hankalina kacokan wajen hada kan mambobin masana’antar ta Kannywood.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Sannan kuma in tafi wajen samo masu hannu da shuni domin su zo su zuba hannayen jarinsu a wannan masana’antar, zaka ga da dama mutane na sha’war zuba hannayen jarinsu a wannan masana’antar amma ba su san yadda za su yi ba ko kuma hanyoyin da za su bi wajen ganin ba su yi asarar kudadensu da su ka zuba a harkar ba.

Daga karshe Alhaji Dan Asabe ya shawarci matasa mata da maza da ke da sha’awar shigowa wannan masana’antar domin su fara harkar fim a kan duk wanda zai shigo ya tabbatar da cewar zai iya hakuri har zuwa lokacin da Allah zai nufi ya samu daukaka, domin kuwa a dare daya ba zai samu abin da yake so ba dole sai ya jajirce ya kuma yi hakuri kamar yadda wadanda yake gani sun samu daukaka suka yi kafin shima ya zama wani abu a Kannywood.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FimHausaHausa Fim
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Faransa Sun Gudanar Da Taron Tattaunawa Bisa Matsayin Koli Karo Na 26 

Next Post

Yadda Wasan Manchester Derby Ya Kaya A Etihad 

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

5 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

2 weeks ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

3 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

4 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Yadda Wasan Manchester Derby Ya Kaya A Etihad 

Yadda Wasan Manchester Derby Ya Kaya A Etihad 

LABARAI MASU NASABA

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.