• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Rage Makin Shiga Jami’a Zai Yi Tasiri Wajen Samun Gurbin Karatu A Jami’o’in Nijeriya?

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Ra'ayoyi
0
Ko Rage Makin Shiga Jami’a Zai Yi Tasiri Wajen Samun Gurbin Karatu A Jami’o’in Nijeriya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar shirya jarabawar shiga jami’o’i ta kasa (JAMB) ta amince da rage makin shiga jami’a zuwa 140 ko fiye da haka, a matsayin shi ne maki mafi kankantar da za a iya samun gurbin karatu jami’a ga wanda ya mallaka a shekarar karatu ta 2022/23 ta shiga jami’oi a fadin tarayyar Nijeriya.

Shugaban hukumar JAMB, Farfesa Is-hak Oloyede ne ya bayyana haka lokacin da yake jawabi yayin da ake kaddamar da tsarin yadda al’amarin samun gurbin karatu na manyan makaratu zai kasance tare da ba da lambar karramawa da ya gudana a Abuja.

  • Karin Kudin Wuta: Akwai Fargabar Korar Miliyoyin Ma’aikata

Oloyede ya ce maki 100 shi aka amince a matsayin mafi karancin maki ga wadanda ke bukatar zuwa makarantun fasaha da kimiyya da kuma kwalejojin ilmi. Wannan yana nuna ba an tilasta wa makarantun sai sun amince da hakan ba, suna iya kara nasu amma kar abin ya wuce misali.

Haka nan ma ya ce dole ne su manyan makarantu su tabbatar suna bin ka’idar da aka bayyana a matsayin yadda za su tabbatar da hakan lokacin da suke duba takardun dalibai masu bukatar shuga makarantunsu.

“Dukkan makarantu abu mafi kyau gare su shi ne na tabbatar da suna bin ka’idarta maki 140 wanda dole a same shi kafin samun damar zuwa jami’a. Wannan na nuna cewa babu jami’ar da za ta amince da kasa da maki 140.

Labarai Masu Nasaba

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

“Ga jami’o’i 15 masu zaman kansu da suka bukaci tsakanin maki 120 da 130, su gane da cewa shi al’amarin maki 140 abin ya tsaya matsayin doka ka da a karya ta.

“Ba za a taba amincewa masu da maki 139, ba za a amince da hakan ba don haka a tabbatar da ana bin dokar sau da kafa yadda aka tanada “.

Wannan sabon tsarin kamar yadda hukumar ta bayyana zai ba masu son rubuta jarabawar su rubuta a wayiyionsu na tafi da gidanka.

Oloyede ya kara jaddada cewa hukumar tana kashe makudan kudade lokacin yin jarabawar shiga jami’o’I, wannan shi ya sa aka bullo da wannan sabon tsarin.

“Muna kallon abin da ya zarce tsari na BOYD, wani tsari ne da daliban da za su rubuta jarabawar su kawo wayoyinsu na tafi da gida. Tsarin yana rage yawan kudaden da ake kashewa, amma bai taimaka wa fasahar ilmi ta zamani. Za a kafa hukumar da za ta rika hukunta wadanda suka aikata laifi lokacin jarabawar da za a bullo da ita ta wayoyin tafi da gidanka.

Ya ci gaba da cewa, “Za mu samu hadin gwiwa da jami’an tsaro daban- daban kan aikata laifin da ya shafi fasahar sadarwa ta zamani lokacin gudanar da jarrabawar da za mu rika daukar nauyinsu saboda suna da masaniyar kan yadda dalibai suke aikata laifin.

“Haka nan ma yadda ake yin rajista lokacin da aka bude damar yin hakan, saboda a yi maganin yadda ake cuta lokacin da ake yin rajisatar.

Ga jarrabawar shiga jami’oi ta shekarar 2023, Oloyede ya bayyana cewar Umeh Nkechinyere ita ce wadda ta fi kowa kwazo daga cikin wadanda suka rubuta jarrabawar da maki 360.

Daga karshe hukumar ta gabatar da mutane 10 da suka fi kowa hazaka daga cikinsu akwai Aguele Stephen mai maki 358 da Ositade Oluwafemi mai maki 358 da Gbolahan Ayinde mai maki 357 da John Fulfilment mai maki 356 da kuma Chimdubem Ugonna mai maki 355.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afrika Ya Gabatar Da Damarmaki Ga DRC

Next Post

Sin Ta Yi Kira Da A Samar Da Yanayin Shawo Kan Rikicin Ukraine Baki Daya

Related

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

2 months ago
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

6 months ago
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

7 months ago
Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya
Ra'ayoyi

Shekara 64 Da Samun ‘Yanci: Maimakon Biki, Jajantawa Ya Kamata A Yi – ‘Yan Nijeriya

7 months ago
Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
Ra'ayoyi

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

7 months ago
Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai
Ra'ayoyi

Dauda Lawal A Shekara 59: Mai Gidana Wanda Bai Da Jiji Da Kai

8 months ago
Next Post
Sin Ta Yi Kira Da A Samar Da Yanayin Shawo Kan Rikicin Ukraine Baki Daya

Sin Ta Yi Kira Da A Samar Da Yanayin Shawo Kan Rikicin Ukraine Baki Daya

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.