ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Rage Makin Shiga Jami’a Zai Yi Tasiri Wajen Samun Gurbin Karatu A Jami’o’in Nijeriya?

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
JAMB

Hukumar shirya jarabawar shiga jami’o’i ta kasa (JAMB) ta amince da rage makin shiga jami’a zuwa 140 ko fiye da haka, a matsayin shi ne maki mafi kankantar da za a iya samun gurbin karatu jami’a ga wanda ya mallaka a shekarar karatu ta 2022/23 ta shiga jami’oi a fadin tarayyar Nijeriya.

Shugaban hukumar JAMB, Farfesa Is-hak Oloyede ne ya bayyana haka lokacin da yake jawabi yayin da ake kaddamar da tsarin yadda al’amarin samun gurbin karatu na manyan makaratu zai kasance tare da ba da lambar karramawa da ya gudana a Abuja.

  • Karin Kudin Wuta: Akwai Fargabar Korar Miliyoyin Ma’aikata

Oloyede ya ce maki 100 shi aka amince a matsayin mafi karancin maki ga wadanda ke bukatar zuwa makarantun fasaha da kimiyya da kuma kwalejojin ilmi. Wannan yana nuna ba an tilasta wa makarantun sai sun amince da hakan ba, suna iya kara nasu amma kar abin ya wuce misali.

ADVERTISEMENT

Haka nan ma ya ce dole ne su manyan makarantu su tabbatar suna bin ka’idar da aka bayyana a matsayin yadda za su tabbatar da hakan lokacin da suke duba takardun dalibai masu bukatar shuga makarantunsu.

“Dukkan makarantu abu mafi kyau gare su shi ne na tabbatar da suna bin ka’idarta maki 140 wanda dole a same shi kafin samun damar zuwa jami’a. Wannan na nuna cewa babu jami’ar da za ta amince da kasa da maki 140.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

“Ga jami’o’i 15 masu zaman kansu da suka bukaci tsakanin maki 120 da 130, su gane da cewa shi al’amarin maki 140 abin ya tsaya matsayin doka ka da a karya ta.

“Ba za a taba amincewa masu da maki 139, ba za a amince da hakan ba don haka a tabbatar da ana bin dokar sau da kafa yadda aka tanada “.

Wannan sabon tsarin kamar yadda hukumar ta bayyana zai ba masu son rubuta jarabawar su rubuta a wayiyionsu na tafi da gidanka.

Oloyede ya kara jaddada cewa hukumar tana kashe makudan kudade lokacin yin jarabawar shiga jami’o’I, wannan shi ya sa aka bullo da wannan sabon tsarin.

“Muna kallon abin da ya zarce tsari na BOYD, wani tsari ne da daliban da za su rubuta jarabawar su kawo wayoyinsu na tafi da gida. Tsarin yana rage yawan kudaden da ake kashewa, amma bai taimaka wa fasahar ilmi ta zamani. Za a kafa hukumar da za ta rika hukunta wadanda suka aikata laifi lokacin jarabawar da za a bullo da ita ta wayoyin tafi da gidanka.

Ya ci gaba da cewa, “Za mu samu hadin gwiwa da jami’an tsaro daban- daban kan aikata laifin da ya shafi fasahar sadarwa ta zamani lokacin gudanar da jarrabawar da za mu rika daukar nauyinsu saboda suna da masaniyar kan yadda dalibai suke aikata laifin.

“Haka nan ma yadda ake yin rajista lokacin da aka bude damar yin hakan, saboda a yi maganin yadda ake cuta lokacin da ake yin rajisatar.

Ga jarrabawar shiga jami’oi ta shekarar 2023, Oloyede ya bayyana cewar Umeh Nkechinyere ita ce wadda ta fi kowa kwazo daga cikin wadanda suka rubuta jarrabawar da maki 360.

Daga karshe hukumar ta gabatar da mutane 10 da suka fi kowa hazaka daga cikinsu akwai Aguele Stephen mai maki 358 da Ositade Oluwafemi mai maki 358 da Gbolahan Ayinde mai maki 357 da John Fulfilment mai maki 356 da kuma Chimdubem Ugonna mai maki 355.

JAMB
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Sin Ta Yi Kira Da A Samar Da Yanayin Shawo Kan Rikicin Ukraine Baki Daya

Sin Ta Yi Kira Da A Samar Da Yanayin Shawo Kan Rikicin Ukraine Baki Daya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.