ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Rage Makin Shiga Jami’a Zai Yi Tasiri Wajen Samun Gurbin Karatu A Jami’o’in Nijeriya?

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
JAMB

Hukumar shirya jarabawar shiga jami’o’i ta kasa (JAMB) ta amince da rage makin shiga jami’a zuwa 140 ko fiye da haka, a matsayin shi ne maki mafi kankantar da za a iya samun gurbin karatu jami’a ga wanda ya mallaka a shekarar karatu ta 2022/23 ta shiga jami’oi a fadin tarayyar Nijeriya.

Shugaban hukumar JAMB, Farfesa Is-hak Oloyede ne ya bayyana haka lokacin da yake jawabi yayin da ake kaddamar da tsarin yadda al’amarin samun gurbin karatu na manyan makaratu zai kasance tare da ba da lambar karramawa da ya gudana a Abuja.

  • Karin Kudin Wuta: Akwai Fargabar Korar Miliyoyin Ma’aikata

Oloyede ya ce maki 100 shi aka amince a matsayin mafi karancin maki ga wadanda ke bukatar zuwa makarantun fasaha da kimiyya da kuma kwalejojin ilmi. Wannan yana nuna ba an tilasta wa makarantun sai sun amince da hakan ba, suna iya kara nasu amma kar abin ya wuce misali.

ADVERTISEMENT

Haka nan ma ya ce dole ne su manyan makarantu su tabbatar suna bin ka’idar da aka bayyana a matsayin yadda za su tabbatar da hakan lokacin da suke duba takardun dalibai masu bukatar shuga makarantunsu.

“Dukkan makarantu abu mafi kyau gare su shi ne na tabbatar da suna bin ka’idarta maki 140 wanda dole a same shi kafin samun damar zuwa jami’a. Wannan na nuna cewa babu jami’ar da za ta amince da kasa da maki 140.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

“Ga jami’o’i 15 masu zaman kansu da suka bukaci tsakanin maki 120 da 130, su gane da cewa shi al’amarin maki 140 abin ya tsaya matsayin doka ka da a karya ta.

“Ba za a taba amincewa masu da maki 139, ba za a amince da hakan ba don haka a tabbatar da ana bin dokar sau da kafa yadda aka tanada “.

Wannan sabon tsarin kamar yadda hukumar ta bayyana zai ba masu son rubuta jarabawar su rubuta a wayiyionsu na tafi da gidanka.

Oloyede ya kara jaddada cewa hukumar tana kashe makudan kudade lokacin yin jarabawar shiga jami’o’I, wannan shi ya sa aka bullo da wannan sabon tsarin.

“Muna kallon abin da ya zarce tsari na BOYD, wani tsari ne da daliban da za su rubuta jarabawar su kawo wayoyinsu na tafi da gida. Tsarin yana rage yawan kudaden da ake kashewa, amma bai taimaka wa fasahar ilmi ta zamani. Za a kafa hukumar da za ta rika hukunta wadanda suka aikata laifi lokacin jarabawar da za a bullo da ita ta wayoyin tafi da gidanka.

Ya ci gaba da cewa, “Za mu samu hadin gwiwa da jami’an tsaro daban- daban kan aikata laifin da ya shafi fasahar sadarwa ta zamani lokacin gudanar da jarrabawar da za mu rika daukar nauyinsu saboda suna da masaniyar kan yadda dalibai suke aikata laifin.

“Haka nan ma yadda ake yin rajista lokacin da aka bude damar yin hakan, saboda a yi maganin yadda ake cuta lokacin da ake yin rajisatar.

Ga jarrabawar shiga jami’oi ta shekarar 2023, Oloyede ya bayyana cewar Umeh Nkechinyere ita ce wadda ta fi kowa kwazo daga cikin wadanda suka rubuta jarrabawar da maki 360.

Daga karshe hukumar ta gabatar da mutane 10 da suka fi kowa hazaka daga cikinsu akwai Aguele Stephen mai maki 358 da Ositade Oluwafemi mai maki 358 da Gbolahan Ayinde mai maki 357 da John Fulfilment mai maki 356 da kuma Chimdubem Ugonna mai maki 355.

JAMB
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Sin Ta Yi Kira Da A Samar Da Yanayin Shawo Kan Rikicin Ukraine Baki Daya

Sin Ta Yi Kira Da A Samar Da Yanayin Shawo Kan Rikicin Ukraine Baki Daya

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026
“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

“Ajin Tashar Sararin Samaniya Na Hong Kong Da Macau” Ya Kara Wa Matasa Sha’awar Kimiyya Da Karfafa Kishin Kasa

September 9, 2026
’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

’Yansanda Sun Cafke Matar Da Ta Kwara Wa Maƙociyarta Tafasasshen Ruwan Zafi A Abuja

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.