• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Talakawa Na Amfana Da Yawaitar Sauya Shekar ’Yan Siyasa?

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
in Rahotonni
0
Ko Talakawa Na Amfana Da Yawaitar Sauya Shekar ’Yan Siyasa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

Sauyawa, canzawa, da dai sauran wadansu kalmomi da suke bada ma’anar barin wani abu zuwa wani akwai dalilin ko dalilan da suke sa ana yin hakan, idan aka kalli ‘yan siyasa suke yi lokacin da aka shiga Kaka ko kuma hulotin siyasa.

Amma dai babbar magana ita ce lokuta da yawa su ‘yan siyasa sun fi yin hakan musamman ma idan lokacin babban zabe ya fara karatowa.

  • CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Murnar Tsakiyar Yanayin Kaka Ta Yin Amfani Da AlAdun Haduwar Iyalai
  • ’Yan Bindiga Sun Saki Mutane 43 Da Suka Sace A Masallaci, Sun Kashe Daya A Zamfara

Sai dai kuma da akwai rashin akidar siyasa wadda ita ce ke sa wasu ‘yan siyasa suke yin hakan abin ya hada da shi wani ko su wasu ‘yan siyasar bata Talakawa suke yi ba, suna duba kansu tun a karon farko.
Wasu daga cikin masu irin wannan akidar idan dai suka nemi wani mukami a siyasa basu samu ba.
To shikenan sai su yanke shawarar barin jam’iyyar siyasar da, aka san suna cikin ta tun shekara da shekaru su kuma wata tare da fatan wankin hula ba zai kai su zuwa dare ba.
Idan ana maganar akidar siyasa ita ce ko mai runtsi,ko wuya ko dadi ,a kada a raya kar mutum ya bar jam’iyyar da yake.
Wannan ana iya tunawa da Shugabannin siyasar jamhuriyya ta farko irin salon siyasa, da akidar da kowannen su yake da ita, bai fa barinta saboda wani dalili na kashin kansa kawai. Yana kallon al’ummar sa ne.
A Jamhuriyya ta farko irin jam’iyyun da suke tasiri sun hada da NPC, NCNC, NEPU, AG, sanin kowa ne suna da akida wadda suka yi amfani da ita.
Shugabanni kamarsu Marigayi Sir Abubakar Tafawa Balewa, Dakta Nnamdi Azikwe, Firimiya Ahmadu Bello Sardauna, Samuel Ladoke Akintola, Chif K.O Mbadwe, Malam Aminu Kano, Sir Kasim, Chif Obafemi Awolowa.
Babu wanda ya bar jam’iyyar da aka san shi da ita zuwa wata. Da haka haraka shigo jamhuriyya ta biyu jam’iyyu 1979 zuwa 1983 UPN, NPN, GNPP, PRP, NPP, hakanan suka tafiyar da al’amuran siyasar nasu tare da akida.
Bayan tsaikon da aka samu daga watan Disamba na shekarar 1983 zuwa shekarar 1999 da aka samu dogon lokacin da ba a yi siyasa ba, sabbin jam’iyyun da suka kasance sune ACN, PDP, APP wadda daga baya ta koma ANPP, APGA, da dai sauran jam’iyyu. Lokacin aka tsayar da Buhari dantakarar Shugaban kasa 2015 da bayan an zabe shi abubuwa da yawa sun faru, musamman masu nasaba da sauya jam’iyya zuwa wata da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bar jam’iyyar PDP ne ya koma APC can ma da bukatar sa bata samu ba ya kara komawa PDP, sannu a hankali shi ma ya barta domin bukatarsa ta kasancewa dan takara ya koma NNPP.
Kamar kunbo kamar katanta shi ma Sanata Ibrahim Shekarau ya bar PDP zuwa APC, sai NNPP har daga karshe dai ya sake komawa PDP.
Kamar dai dan takarar shugaban kasa na PDP Atiku Abubakar haka ya bar PDP zuwa APC da yake abin yaki ci yaki cinyewa sai ya koma PDP.
Idan dai ba a manta ba Sanata Bukola Saraki da Tsohon Ministan Sufuri Chibuke Rotimi Amechi, tsohon shugaban majalisar wakilai kafin ya zama gwamna Aminu Waziri Tambuwal da sauran wasu gaggan ‘yan siyasa suna irin wannan sauye- sauyen jam’iyya.
Shi sauyin jam’iyya kowa yana da na shi ra’ayi, wani manufar shi bai samun aiwatarwa, wani shugabanci yake kwadayi, wani taimakawa al’ummarsa yake son yi.
Ya lura kuma inda yake ba zai cimma burin shi ba sai ya sauya jam’iyya, yayin da wasu suke shiga da sa a wasu gara jiya da yau haka dai al’amarin yake kasancewa.
Koda yake dai shi wannan al’amari na sauya jam’iyyar siyasar da wasu ‘yan siyasa ko shakka babu suna kwashewa da mara be domin kuwa idan ba su samun hakan, ko mafarkin yin hakan ma ba za su yi ba.
Sun kuma san suna da magoya baya ne wadanda duk inda suka nufa suna binsu, kamar dai irin manyan ‘yansiyasa wadanda Talakawa ke karuwa da su.
Muna iya duba Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya taimakawa ‘ya’yan Talakawa lokacin da yake gwamnan Jihar Kano har ma daya rike mukamin Minista da kuma Sanata, hakan shi ma Sanata Ibrahim Shekarau tare da sauran ‘yan siyasa kowa ya san irin gudunmawar da yake ba magoya bayansa ko lokacin siyasa, ko kuma akasin hakan taimaka masu yake yi.
Irin haka ce ta sa wasu ‘yan siyasar sun san irin amfanar da suke samu daga wurin ‘yan siyasa wadanda suke goya ma baya, duk abinda suka ce ma Talakawan su yi a shirye suke su yi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ShugabbaniSiyasaTalakawaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Noman Auduga Na Ci Gaba Da Fuskantar Matsaloli – Cewar Masana

Next Post

Zabar Musulmi Da Musulmi Da APC Ta Yi Ba Illa Ba Ce -Hon. Auwalu Ladan Garba

Related

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

19 hours ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

7 days ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

7 days ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

2 months ago
Next Post
Zabar Musulmi Da Musulmi Da APC Ta Yi Ba Illa Ba Ce -Hon. Auwalu Ladan Garba

Zabar Musulmi Da Musulmi Da APC Ta Yi Ba Illa Ba Ce -Hon. Auwalu Ladan Garba

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.