• Leadership Hausa
Tuesday, March 21, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Talakawa Na Amfana Da Yawaitar Sauya Shekar ’Yan Siyasa?

by Idris Aliyu Daudawa
6 months ago
in Rahotonni
0
Ko Talakawa Na Amfana Da Yawaitar Sauya Shekar ’Yan Siyasa?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

NLC Na Shirin Shiga Yajin Aiki Kan Karancin Man Fetur Da Takardun Kudi 

Gudummawar Hajiya Hadiza Bala Usman Wajen Bunkasa Rayuwar Matan Nijeriya

Sauyawa, canzawa, da dai sauran wadansu kalmomi da suke bada ma’anar barin wani abu zuwa wani akwai dalilin ko dalilan da suke sa ana yin hakan, idan aka kalli ‘yan siyasa suke yi lokacin da aka shiga Kaka ko kuma hulotin siyasa.

Amma dai babbar magana ita ce lokuta da yawa su ‘yan siyasa sun fi yin hakan musamman ma idan lokacin babban zabe ya fara karatowa.

  • CMG Za Ta Gabatar Da Bikin Murnar Tsakiyar Yanayin Kaka Ta Yin Amfani Da AlAdun Haduwar Iyalai
  • ’Yan Bindiga Sun Saki Mutane 43 Da Suka Sace A Masallaci, Sun Kashe Daya A Zamfara

Sai dai kuma da akwai rashin akidar siyasa wadda ita ce ke sa wasu ‘yan siyasa suke yin hakan abin ya hada da shi wani ko su wasu ‘yan siyasar bata Talakawa suke yi ba, suna duba kansu tun a karon farko.
Wasu daga cikin masu irin wannan akidar idan dai suka nemi wani mukami a siyasa basu samu ba.
To shikenan sai su yanke shawarar barin jam’iyyar siyasar da, aka san suna cikin ta tun shekara da shekaru su kuma wata tare da fatan wankin hula ba zai kai su zuwa dare ba.
Idan ana maganar akidar siyasa ita ce ko mai runtsi,ko wuya ko dadi ,a kada a raya kar mutum ya bar jam’iyyar da yake.
Wannan ana iya tunawa da Shugabannin siyasar jamhuriyya ta farko irin salon siyasa, da akidar da kowannen su yake da ita, bai fa barinta saboda wani dalili na kashin kansa kawai. Yana kallon al’ummar sa ne.
A Jamhuriyya ta farko irin jam’iyyun da suke tasiri sun hada da NPC, NCNC, NEPU, AG, sanin kowa ne suna da akida wadda suka yi amfani da ita.
Shugabanni kamarsu Marigayi Sir Abubakar Tafawa Balewa, Dakta Nnamdi Azikwe, Firimiya Ahmadu Bello Sardauna, Samuel Ladoke Akintola, Chif K.O Mbadwe, Malam Aminu Kano, Sir Kasim, Chif Obafemi Awolowa.
Babu wanda ya bar jam’iyyar da aka san shi da ita zuwa wata. Da haka haraka shigo jamhuriyya ta biyu jam’iyyu 1979 zuwa 1983 UPN, NPN, GNPP, PRP, NPP, hakanan suka tafiyar da al’amuran siyasar nasu tare da akida.
Bayan tsaikon da aka samu daga watan Disamba na shekarar 1983 zuwa shekarar 1999 da aka samu dogon lokacin da ba a yi siyasa ba, sabbin jam’iyyun da suka kasance sune ACN, PDP, APP wadda daga baya ta koma ANPP, APGA, da dai sauran jam’iyyu. Lokacin aka tsayar da Buhari dantakarar Shugaban kasa 2015 da bayan an zabe shi abubuwa da yawa sun faru, musamman masu nasaba da sauya jam’iyya zuwa wata da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bar jam’iyyar PDP ne ya koma APC can ma da bukatar sa bata samu ba ya kara komawa PDP, sannu a hankali shi ma ya barta domin bukatarsa ta kasancewa dan takara ya koma NNPP.
Kamar kunbo kamar katanta shi ma Sanata Ibrahim Shekarau ya bar PDP zuwa APC, sai NNPP har daga karshe dai ya sake komawa PDP.
Kamar dai dan takarar shugaban kasa na PDP Atiku Abubakar haka ya bar PDP zuwa APC da yake abin yaki ci yaki cinyewa sai ya koma PDP.
Idan dai ba a manta ba Sanata Bukola Saraki da Tsohon Ministan Sufuri Chibuke Rotimi Amechi, tsohon shugaban majalisar wakilai kafin ya zama gwamna Aminu Waziri Tambuwal da sauran wasu gaggan ‘yan siyasa suna irin wannan sauye- sauyen jam’iyya.
Shi sauyin jam’iyya kowa yana da na shi ra’ayi, wani manufar shi bai samun aiwatarwa, wani shugabanci yake kwadayi, wani taimakawa al’ummarsa yake son yi.
Ya lura kuma inda yake ba zai cimma burin shi ba sai ya sauya jam’iyya, yayin da wasu suke shiga da sa a wasu gara jiya da yau haka dai al’amarin yake kasancewa.
Koda yake dai shi wannan al’amari na sauya jam’iyyar siyasar da wasu ‘yan siyasa ko shakka babu suna kwashewa da mara be domin kuwa idan ba su samun hakan, ko mafarkin yin hakan ma ba za su yi ba.
Sun kuma san suna da magoya baya ne wadanda duk inda suka nufa suna binsu, kamar dai irin manyan ‘yansiyasa wadanda Talakawa ke karuwa da su.
Muna iya duba Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya taimakawa ‘ya’yan Talakawa lokacin da yake gwamnan Jihar Kano har ma daya rike mukamin Minista da kuma Sanata, hakan shi ma Sanata Ibrahim Shekarau tare da sauran ‘yan siyasa kowa ya san irin gudunmawar da yake ba magoya bayansa ko lokacin siyasa, ko kuma akasin hakan taimaka masu yake yi.
Irin haka ce ta sa wasu ‘yan siyasar sun san irin amfanar da suke samu daga wurin ‘yan siyasa wadanda suke goya ma baya, duk abinda suka ce ma Talakawan su yi a shirye suke su yi.

Tags: ShugabbaniSiyasaTalakawaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Noman Auduga Na Ci Gaba Da Fuskantar Matsaloli – Cewar Masana

Next Post

Zabar Musulmi Da Musulmi Da APC Ta Yi Ba Illa Ba Ce -Hon. Auwalu Ladan Garba

Related

NLC Na Shirin Shiga Yajin Aiki Kan Karancin Man Fetur Da Takardun Kudi 
Rahotonni

NLC Na Shirin Shiga Yajin Aiki Kan Karancin Man Fetur Da Takardun Kudi 

7 days ago
Gudummawar Hajiya Hadiza Bala Usman Wajen Bunkasa Rayuwar Matan Nijeriya
Rahotonni

Gudummawar Hajiya Hadiza Bala Usman Wajen Bunkasa Rayuwar Matan Nijeriya

1 week ago
Sin Ta Taya Murnar Bola Tinubu Ya Zama Shugaban Nijeriya
Rahotonni

An Fara Zawarcin Mukaman Siyasa A Gwamnatin Tinubu

2 weeks ago
Zaben Gwamnoni: Jihohin Da Za A Fafata Mai Tsanani
Rahotonni

Zaben Gwamnoni: Jihohin Da Za A Fafata Mai Tsanani

2 weeks ago
‘Yansanda Sun Cafke Mutum 50 Kan Satar Kaya Lokacin Da Gobara Ke Cin Kasuwar Monday Market A Borno
Rahotonni

Waiwaye: Konewar Babbar Kasuwar Maiduguri A Shekarar 1979 Da Sake Gina Ta Da Aka Yi A 1983

2 weeks ago
Sakamakon Zaben Shugaban Kasa Daga Kananan Hukumomin Jihar Bauchi 
Rahotonni

Manyan Abubuwa Takwas Da Suka Girgiza Zaben Shugaban Kasa Na 2023

3 weeks ago
Next Post
Zabar Musulmi Da Musulmi Da APC Ta Yi Ba Illa Ba Ce -Hon. Auwalu Ladan Garba

Zabar Musulmi Da Musulmi Da APC Ta Yi Ba Illa Ba Ce -Hon. Auwalu Ladan Garba

LABARAI MASU NASABA

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

Jihar Zamfara: Dauda Lawal Dare Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamna Matawalle Na APC

March 21, 2023
An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanin Magabata Da Xi Jinping Ke So” Na 2 Da Harshen Rashanci 

An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanin Magabata Da Xi Jinping Ke So” Na 2 Da Harshen Rashanci 

March 20, 2023
Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha Vladimir Putin

Shugaban Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha Vladimir Putin

March 20, 2023
Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

Ramadan: Shehu Isma’ila Mai Diwani Ya Buɗe Tafsirin Alƙur’ani A Kaduna

March 20, 2023
Firaministan Kasar Djibouti Ya Mikawa Tawagar Jiyya Ta Kasar Sin Lambar Yabo

Firaministan Kasar Djibouti Ya Mikawa Tawagar Jiyya Ta Kasar Sin Lambar Yabo

March 20, 2023
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

An Sace Baturen Zabe Akan Hanyarsa Ta Zuwa Cibiyar Tattara Sakamakon Zabe A Zamfara

March 20, 2023
Dangantakar Sin Da Rasha Ta Bayyana “Hanyar Da Ta Dace Ta Cudanya Tsakanin Kasa Da Kasa”

Dangantakar Sin Da Rasha Ta Bayyana “Hanyar Da Ta Dace Ta Cudanya Tsakanin Kasa Da Kasa”

March 20, 2023
Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno

Gwamna Zulum Ya Sake Lashe Zaben Gwamna A Jihar Borno

March 20, 2023
An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba

An Kashe ‘Yansanda 2, Da Dama Sun Samu Raunuka A Wata Arangama Da Sojoji A Taraba

March 20, 2023
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Sauran Kasashen Yammacin Duniya Da Su Gaggauta Dage Takunkumin Kan Bangare Daya

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Da Sauran Kasashen Yammacin Duniya Da Su Gaggauta Dage Takunkumin Kan Bangare Daya

March 20, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.