• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun jiha da ke zamanta a Owerri, babban birnin jihar Imo, ta yanke wa tsohon kwamishinan sufuri a karkashin gwamnatin Rochas Okorocha, Laz Okoroafor-Anyanwu, hukuncin daurin shekaru uku a gidan yari, bayan da aka same shi da laifukan da suka shafi zamba da sata.

Da ta ke yanke hukuncin, alkalin kotun, Mai shari’a K.A Lewanya, ya ce Okoroafor-Anyanwu an same shi da laifin karkatar da Naira miliyan 180 na kudaden jihar zuwa asusun wani kamfani mai zaman kansa.

  • Hukumar Kula Da Aikin Makaurata Ta Kasar Sin Ta Daidaita Manufofin Ba Da Iznin Shigo Kasar
  • Birnin Beijing Zai Kara Yawan Lambunan Shakatawa

Alkalin ta ce ya kasance babban mai hannun jari a kamfanin.

A cewar mai shari’a, Okoroafor-Anyanwu an kuma same shi da laifin karya dokar siyan kaya, cin zarafin ofis, da kuma yin amfani da ofishinsa wajen samun tagomashi da bai dace ba a cikin harkokinsa a lokacin da yake rike da mukamin kwamishina.

Ya ce lauyan Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), Barista Michael Ani, wanda shi ne lauyan mai shigar da kara ya tabbatar da babu shakka cewa lokacin da Okoroafor-Anyanwu yake kwamishinan a tsakanin 2015 zuwa 2019, ya mika zunzurutun kudi har Naira miliyan 100 daga asusun ITC zuwa kamfanin mai zaman kansa mai suna Oma Oil Industries Limited wanda ya sabawa sashe na 12 da 19 na dokar ICPC ta 2020 na ma’aikacin gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Alkalin kotun ta kara da cewa, a irin wannan hali, Okoroafor-Anyanwu ya sanya hannu a kan wasu kudi har Naira miliyan 80 daga asusun gwamnati kai tsaye zuwa asusun kamfaninsa mai zaman kansa kan cewa zai sayo wasu motoci don gudanar da ayyuka ba tare da bin ka’ida da bin doka da oda na ma’aikatan gwamnati ba.

Ko da yake Okoroafor-Anyanwu ya ki amsa laifinsa, alkalin da ta yanke hukuncin daurin shekara daya a gidan yari ba tare da zabin tara ba.

Alkalin ta kuma yanke hukuncin cewa kudin da aka wawure Naira miliyan 180 da aka samu a asusunsa, a mika su ga Kamfanin Sufuri na Jihar Imo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ImoKotuKwamishina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kula Da Aikin Makaurata Ta Kasar Sin Ta Daidaita Manufofin Ba Da Iznin Shigo Kasar

Next Post

Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin ‘Yan Bindiga

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

37 minutes ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

17 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin ‘Yan Bindiga

Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.