• English
  • Business News
Monday, August 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun jiha da ke zamanta a Owerri, babban birnin jihar Imo, ta yanke wa tsohon kwamishinan sufuri a karkashin gwamnatin Rochas Okorocha, Laz Okoroafor-Anyanwu, hukuncin daurin shekaru uku a gidan yari, bayan da aka same shi da laifukan da suka shafi zamba da sata.

Da ta ke yanke hukuncin, alkalin kotun, Mai shari’a K.A Lewanya, ya ce Okoroafor-Anyanwu an same shi da laifin karkatar da Naira miliyan 180 na kudaden jihar zuwa asusun wani kamfani mai zaman kansa.

  • Hukumar Kula Da Aikin Makaurata Ta Kasar Sin Ta Daidaita Manufofin Ba Da Iznin Shigo Kasar
  • Birnin Beijing Zai Kara Yawan Lambunan Shakatawa

Alkalin ta ce ya kasance babban mai hannun jari a kamfanin.

A cewar mai shari’a, Okoroafor-Anyanwu an kuma same shi da laifin karya dokar siyan kaya, cin zarafin ofis, da kuma yin amfani da ofishinsa wajen samun tagomashi da bai dace ba a cikin harkokinsa a lokacin da yake rike da mukamin kwamishina.

Ya ce lauyan Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), Barista Michael Ani, wanda shi ne lauyan mai shigar da kara ya tabbatar da babu shakka cewa lokacin da Okoroafor-Anyanwu yake kwamishinan a tsakanin 2015 zuwa 2019, ya mika zunzurutun kudi har Naira miliyan 100 daga asusun ITC zuwa kamfanin mai zaman kansa mai suna Oma Oil Industries Limited wanda ya sabawa sashe na 12 da 19 na dokar ICPC ta 2020 na ma’aikacin gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Alkalin kotun ta kara da cewa, a irin wannan hali, Okoroafor-Anyanwu ya sanya hannu a kan wasu kudi har Naira miliyan 80 daga asusun gwamnati kai tsaye zuwa asusun kamfaninsa mai zaman kansa kan cewa zai sayo wasu motoci don gudanar da ayyuka ba tare da bin ka’ida da bin doka da oda na ma’aikatan gwamnati ba.

Ko da yake Okoroafor-Anyanwu ya ki amsa laifinsa, alkalin da ta yanke hukuncin daurin shekara daya a gidan yari ba tare da zabin tara ba.

Alkalin ta kuma yanke hukuncin cewa kudin da aka wawure Naira miliyan 180 da aka samu a asusunsa, a mika su ga Kamfanin Sufuri na Jihar Imo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ImoKotuKwamishina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kula Da Aikin Makaurata Ta Kasar Sin Ta Daidaita Manufofin Ba Da Iznin Shigo Kasar

Next Post

Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin ‘Yan Bindiga

Related

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

7 hours ago
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
Manyan Labarai

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

12 hours ago
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
Manyan Labarai

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

14 hours ago
ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja
Manyan Labarai

An Maka Gwamnatin Neja Da NBC A Kotu Kan Barazanar Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM

17 hours ago
NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja
Manyan Labarai

NDLEA Ta Cafke Masu Baburan Da Ke Kai Saƙon Muggan Ƙwayoyi A Abuja

20 hours ago
An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

2 days ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin ‘Yan Bindiga

Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Ko MaÆ™iyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko MaÆ™iyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga ÆŠan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga ÆŠan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.