• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Daure Tsohon Kwamishina Shekara 3 Kan Almundahanar Miliyan 180 A Imo
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun jiha da ke zamanta a Owerri, babban birnin jihar Imo, ta yanke wa tsohon kwamishinan sufuri a karkashin gwamnatin Rochas Okorocha, Laz Okoroafor-Anyanwu, hukuncin daurin shekaru uku a gidan yari, bayan da aka same shi da laifukan da suka shafi zamba da sata.

Da ta ke yanke hukuncin, alkalin kotun, Mai shari’a K.A Lewanya, ya ce Okoroafor-Anyanwu an same shi da laifin karkatar da Naira miliyan 180 na kudaden jihar zuwa asusun wani kamfani mai zaman kansa.

  • Hukumar Kula Da Aikin Makaurata Ta Kasar Sin Ta Daidaita Manufofin Ba Da Iznin Shigo Kasar
  • Birnin Beijing Zai Kara Yawan Lambunan Shakatawa

Alkalin ta ce ya kasance babban mai hannun jari a kamfanin.

A cewar mai shari’a, Okoroafor-Anyanwu an kuma same shi da laifin karya dokar siyan kaya, cin zarafin ofis, da kuma yin amfani da ofishinsa wajen samun tagomashi da bai dace ba a cikin harkokinsa a lokacin da yake rike da mukamin kwamishina.

Ya ce lauyan Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), Barista Michael Ani, wanda shi ne lauyan mai shigar da kara ya tabbatar da babu shakka cewa lokacin da Okoroafor-Anyanwu yake kwamishinan a tsakanin 2015 zuwa 2019, ya mika zunzurutun kudi har Naira miliyan 100 daga asusun ITC zuwa kamfanin mai zaman kansa mai suna Oma Oil Industries Limited wanda ya sabawa sashe na 12 da 19 na dokar ICPC ta 2020 na ma’aikacin gwamnati.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Alkalin kotun ta kara da cewa, a irin wannan hali, Okoroafor-Anyanwu ya sanya hannu a kan wasu kudi har Naira miliyan 80 daga asusun gwamnati kai tsaye zuwa asusun kamfaninsa mai zaman kansa kan cewa zai sayo wasu motoci don gudanar da ayyuka ba tare da bin ka’ida da bin doka da oda na ma’aikatan gwamnati ba.

Ko da yake Okoroafor-Anyanwu ya ki amsa laifinsa, alkalin da ta yanke hukuncin daurin shekara daya a gidan yari ba tare da zabin tara ba.

Alkalin ta kuma yanke hukuncin cewa kudin da aka wawure Naira miliyan 180 da aka samu a asusunsa, a mika su ga Kamfanin Sufuri na Jihar Imo.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ImoKotuKwamishina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Kula Da Aikin Makaurata Ta Kasar Sin Ta Daidaita Manufofin Ba Da Iznin Shigo Kasar

Next Post

Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin ‘Yan Bindiga

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

6 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

8 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

1 day ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

1 day ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

2 days ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin ‘Yan Bindiga

Dan Takarar Gwamnan PDP A Delta Ya Tsallake Rijiya Da Baya Daga Harin 'Yan Bindiga

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.