• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Tarayya ta daya da ke Yola a Jihar Adamawa, karkashin jagorancin mai shari’a A.M. Anka, ta soke zaben fidda gwanin jam’iyyar APC wanda ya samar da Sanata mai wakiltar Adamawa ta tsakiya, Aishatu Dahiru Binani, a matsayin ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar a zaben 2023. 

Mai shari’a Anka ya ce jam’iyyar ba ta da dan takarar gwamna a zaben 2023 a jihar, saboda bai bayar da umarnin sake sake zaben fidda gwani ba.

  • Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira
  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Kafuwar Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Bunkasa Kirkire-Kirkire Da Ilimi Domin Wanzar Da Ci Gaba A Fannin Sufuri

Idan za a iya tunawa cewar Binani ce ta lashe zaben fidda gwanin da aka gudanar a ranar 27 ga watan Mayun 2022, inda ta samu kuri’u 430 wanda ta kayar da abokin hamayyarta Nuhu Ribadu wanda ya samu kuri’u 288; da kuma tsohon gwamnan jihar, Umaru Bindow wanda ya samu kuri’u 103; sai Hon. Abdulrazak Namdas wanda ya samu kuri’u 94, Safari Theman ya samu kuri’u 21, Umar Mustapha ya samu kuri’u 39.

Kotun ta kuma ce jam’iyyar ba za ta shiga zaben gwamna na 2023 ba, saboda haka ta gargadi Sanata Aishatu Dahiru Ahmed Binani da kada ta bayyana kanta a matsayin ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar APC a Jihar Adamawa.

Mai shari’a Anka a lokacin da ya ke yanke hukunci a ranar Juma’a, ya ce an yanke hukuncin ne kan rashin bin ka’idojin jam’iyyar da kuma kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya a zaben fidda gwanin.

Labarai Masu Nasaba

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

Ribadu, wanda ya zo na biyu a zaben fidda gwanin, ya maka ‘yar takarar gwamnan, Aishatu Binani, APC da INEC a gaban kotu.

Ya kuma bayar da shawarar soke zaben fidda gwanin da aka yi, inda ya yi zargin an tafka kura-kurai a lokacin zaben fidda gwanin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaAisha BinaniAPCKotuRibadu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira

Next Post

Kotu Ta Tsare Hamshakin Dankasuwa Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

Related

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA
Manyan Labarai

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

14 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

20 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

1 day ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

1 day ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

1 day ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

2 days ago
Next Post
Kotu Ta Tsare Hamshakin Dankasuwa Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

Kotu Ta Tsare Hamshakin Dankasuwa Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

Nijeriya Na Bukatar Dala Biliyan 10 Kowace Shekara Domin Samun Ingantacciyar Wutar Lantarki — Minista

May 16, 2025
Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

Masu Garkuwa Sun Nemi Miliyan ₦30 Don Sako Shugaban APC A Ondo

May 16, 2025
Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar

May 16, 2025
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

May 16, 2025
Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

May 16, 2025
Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

Abin  Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (1)

May 16, 2025
Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

Rashin Tsaro Da Raba Wa Manoma Kayan Aiki Kan Lokaci Na Baraza Ga Wadata Kasa Da Abinci

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.