ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Rushe Zaben Fidda Gwanin APC A Jihar Adamawa 

by Sadiq
4 years ago
APC

Babbar Kotun Tarayya ta daya da ke Yola a Jihar Adamawa, karkashin jagorancin mai shari’a A.M. Anka, ta soke zaben fidda gwanin jam’iyyar APC wanda ya samar da Sanata mai wakiltar Adamawa ta tsakiya, Aishatu Dahiru Binani, a matsayin ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar a zaben 2023. 

Mai shari’a Anka ya ce jam’iyyar ba ta da dan takarar gwamna a zaben 2023 a jihar, saboda bai bayar da umarnin sake sake zaben fidda gwani ba.

  • Abin Da Ya Sa Manoman Doya A Jihar Taraba Ke Tafka Asarar Miliyoyin Naira
  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Kafuwar Cibiyar Kasa Da Kasa Ta Bunkasa Kirkire-Kirkire Da Ilimi Domin Wanzar Da Ci Gaba A Fannin Sufuri

Idan za a iya tunawa cewar Binani ce ta lashe zaben fidda gwanin da aka gudanar a ranar 27 ga watan Mayun 2022, inda ta samu kuri’u 430 wanda ta kayar da abokin hamayyarta Nuhu Ribadu wanda ya samu kuri’u 288; da kuma tsohon gwamnan jihar, Umaru Bindow wanda ya samu kuri’u 103; sai Hon. Abdulrazak Namdas wanda ya samu kuri’u 94, Safari Theman ya samu kuri’u 21, Umar Mustapha ya samu kuri’u 39.

ADVERTISEMENT

Kotun ta kuma ce jam’iyyar ba za ta shiga zaben gwamna na 2023 ba, saboda haka ta gargadi Sanata Aishatu Dahiru Ahmed Binani da kada ta bayyana kanta a matsayin ‘yar takarar gwamna a jam’iyyar APC a Jihar Adamawa.

Mai shari’a Anka a lokacin da ya ke yanke hukunci a ranar Juma’a, ya ce an yanke hukuncin ne kan rashin bin ka’idojin jam’iyyar da kuma kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya a zaben fidda gwanin.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Ribadu, wanda ya zo na biyu a zaben fidda gwanin, ya maka ‘yar takarar gwamnan, Aishatu Binani, APC da INEC a gaban kotu.

Ya kuma bayar da shawarar soke zaben fidda gwanin da aka yi, inda ya yi zargin an tafka kura-kurai a lokacin zaben fidda gwanin.

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Kotu Ta Tsare Hamshakin Dankasuwa Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

Kotu Ta Tsare Hamshakin Dankasuwa Kan Zargin Yi Wa Karamar Yarinya Fyade

LABARAI MASU NASABA

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.