• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna, ta soke zaben fidda gwanin da jam’iyyar PDP ta gudanar a mazabar Kaduna ta tsakiya sakamakon wasu kurakurai. 

Kotun ta umarci jam’iyyar PDP da ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani na dan takarar Sanata na jam’iyyar a cikin kwanaki 14.

  • An Mayar Da Tubabbun Mayakan Boko Haram 3,500 Unguwanninsu A Jihar Borno
  • Rashin Tsaro: Buhari Ya Kalubalanci ‘Yansanda A Kan Matsalar Tsaro 

Mai shari’a Muhammed Garba Umar na babbar kotun tarayya da ke Kaduna, wanda ya yanke hukunci a ranar Laraba a kan shari’ar ya ce “Duk korafe-korafen da mai shigar da karar ya yi na da yawa, haka ma hukuncin da INEC ta yanke na gudanar da sabon zaben fidda gwani da ba a yi ba daga baya, kamar yadda sakamakon ya gudana, ikirarin da wanda ake tuhuma ya yi watsi da shi.”

Mai shigar da karar, Usman Ibrahim, ta bakin lauyansa, Samuel Atung, (SAN), ya garzaya kotu yana kalubalantar fitowar Lawal Adamu a kan rashin kuri’ar da aka kada masa, inda ya roki kotun da ta rushe wannan zaben tare da bai wa duk wani mai bukata dama daidai gwargwado don gwada farin jininsa.

Atung ya bayar da hujjar cewa wanda yake karewa yana da faifan bidiyo da bayanan da suka nuna cewa wakilai sun kada kuri’a wadanda sakamakon shari’ar da ya yi nuni da su shi ne rushe sakamakon zaben fidda gwanin da kuma soke sakamakon zaben, inda ya kara da cewa majalisar zartaswar jam’iyyar PDP ta kasa ta nemi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa.

Labarai Masu Nasaba

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

Hukumar INEC ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani kawai don wanda ya karewa ya tattaro mabiyansa zuwa wurin da aka yi zaben a banza.

Lauyan Usman Ibrahim, Samuel Atung, (SAN) da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan yanke hukuncin, ya tabbatar da cewa kotun ta zartar da hukunci ne bayan nazari da ta yi.

Atung ya ce, “Bayan da jam’iyyar PDP ta Kaduna ta tsakiya ta zabi dan takararta a zaben 2023, abokin takararmu ya rubuta koke ga kwamitin daukaka kara na jam’iyyar yana kalubalantar sakamakon zaben.

“Muna da hujjojin bidiyo kan hakan kuma kwamitin ya yi la’akari da rokon da muka gabatar kuma ya mika shawararsa ga kwamitin zaben wanda a cikin hikimarsa ya yi kira da a sake zaben fidda gwanin.

“Jam’iyyar PDP ta rubuta wa INEC wasika, ta sanar da ‘yansandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da sauran masu ruwa da tsaki game da matakin da ta dauka na sake gudanar da zaben fidda gwanin na shiyyar Sanata Kaduna ta tsakiya, wanda abin farin ciki ne.

“Abin takaici a ranar da aka saka, abokin aikinmu, bayan ya tattaro magoya bayansa zuwa wurin da za a sake zaben fidda gwanin, sai aka ce ba za a ci gaba da gudanar da zaben ba saboda yadda mahukuntan suka ba da umarni.

“Mun zo kotu ne muna neman adalci a wannan takin kuma alkali ya yanke hukuncin cewa jam’iyyar ta bi matakin da kwamitin kasa ya dauka sannan ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwanin nan da makonni biyu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaKotuPDPSanataSoke ZabeZaben Fidda Gwani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ziyarar Da Shugabar Tanzaniya Za Ta Kawo Sin Za Ta Bunkasa Alaka Tsakanin Kasashen Biyu Zuwa Wani Sabon Matsayi

Next Post

Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

Related

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

22 hours ago
Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Manyan Labarai

Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya

1 day ago
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

2 days ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

2 days ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

2 days ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

3 days ago
Next Post
Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

LABARAI MASU NASABA

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.