• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotu Ta Soke Zaben Fidda Gwanin PDP A Kaduna Ta Tsakiya, Ta Bada Mako 2 A Sake Wani Zaben
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna, ta soke zaben fidda gwanin da jam’iyyar PDP ta gudanar a mazabar Kaduna ta tsakiya sakamakon wasu kurakurai. 

Kotun ta umarci jam’iyyar PDP da ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani na dan takarar Sanata na jam’iyyar a cikin kwanaki 14.

  • An Mayar Da Tubabbun Mayakan Boko Haram 3,500 Unguwanninsu A Jihar Borno
  • Rashin Tsaro: Buhari Ya Kalubalanci ‘Yansanda A Kan Matsalar Tsaro 

Mai shari’a Muhammed Garba Umar na babbar kotun tarayya da ke Kaduna, wanda ya yanke hukunci a ranar Laraba a kan shari’ar ya ce “Duk korafe-korafen da mai shigar da karar ya yi na da yawa, haka ma hukuncin da INEC ta yanke na gudanar da sabon zaben fidda gwani da ba a yi ba daga baya, kamar yadda sakamakon ya gudana, ikirarin da wanda ake tuhuma ya yi watsi da shi.”

Mai shigar da karar, Usman Ibrahim, ta bakin lauyansa, Samuel Atung, (SAN), ya garzaya kotu yana kalubalantar fitowar Lawal Adamu a kan rashin kuri’ar da aka kada masa, inda ya roki kotun da ta rushe wannan zaben tare da bai wa duk wani mai bukata dama daidai gwargwado don gwada farin jininsa.

Atung ya bayar da hujjar cewa wanda yake karewa yana da faifan bidiyo da bayanan da suka nuna cewa wakilai sun kada kuri’a wadanda sakamakon shari’ar da ya yi nuni da su shi ne rushe sakamakon zaben fidda gwanin da kuma soke sakamakon zaben, inda ya kara da cewa majalisar zartaswar jam’iyyar PDP ta kasa ta nemi hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Hukumar INEC ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwani kawai don wanda ya karewa ya tattaro mabiyansa zuwa wurin da aka yi zaben a banza.

Lauyan Usman Ibrahim, Samuel Atung, (SAN) da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan yanke hukuncin, ya tabbatar da cewa kotun ta zartar da hukunci ne bayan nazari da ta yi.

Atung ya ce, “Bayan da jam’iyyar PDP ta Kaduna ta tsakiya ta zabi dan takararta a zaben 2023, abokin takararmu ya rubuta koke ga kwamitin daukaka kara na jam’iyyar yana kalubalantar sakamakon zaben.

“Muna da hujjojin bidiyo kan hakan kuma kwamitin ya yi la’akari da rokon da muka gabatar kuma ya mika shawararsa ga kwamitin zaben wanda a cikin hikimarsa ya yi kira da a sake zaben fidda gwanin.

“Jam’iyyar PDP ta rubuta wa INEC wasika, ta sanar da ‘yansandan Nijeriya, jami’an tsaron farin kaya da sauran masu ruwa da tsaki game da matakin da ta dauka na sake gudanar da zaben fidda gwanin na shiyyar Sanata Kaduna ta tsakiya, wanda abin farin ciki ne.

“Abin takaici a ranar da aka saka, abokin aikinmu, bayan ya tattaro magoya bayansa zuwa wurin da za a sake zaben fidda gwanin, sai aka ce ba za a ci gaba da gudanar da zaben ba saboda yadda mahukuntan suka ba da umarni.

“Mun zo kotu ne muna neman adalci a wannan takin kuma alkali ya yanke hukuncin cewa jam’iyyar ta bi matakin da kwamitin kasa ya dauka sannan ta sake gudanar da sabon zaben fidda gwanin nan da makonni biyu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaKotuPDPSanataSoke ZabeZaben Fidda Gwani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ziyarar Da Shugabar Tanzaniya Za Ta Kawo Sin Za Ta Bunkasa Alaka Tsakanin Kasashen Biyu Zuwa Wani Sabon Matsayi

Next Post

Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

2 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

14 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

16 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Next Post
Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

Sin Ta Sanar Da Shirin Bunkasa Fasahar VR

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.