• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 3 Hukuncin Kisa Kan Yi Wa Dalibar Jami’a Fyade

by Sadiq
3 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotu ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga mutum uku daga cikin mutum takwas da ake zargi da yin fyade da kashe dalibar Jami’ar Illorin mai shekara 24 a duniya, Olajide Blessing Omowumi, a ranar 2 ga watan Yuni, 2021.

Babbar kotun Jihar Kwara da ke zamanta a Ilorin ce ta yanke wannan hukuncin a ranar Talata.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 
  • Kanu Ya Yi Tur Da Kai Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Kudu Maso Gabas

Mutum uku da aka yanke wa hukuncin da wasu da ake zargi Gwamnatin Jihar Kwara ce ta gurfanar da su a gaban kotun cikin kara mai lamba KWS/33c/c/2021 dauke da tuhume-tuhume guda 11 da suka hada da fashi da makami, mallakar Malamai ba bisa ka’ida ba da kuma fyade hadi da sauran tuhume-tuhume.

A hukuncin da mai shari’a Ibrahim Adebayo Yusuf, ya yanke ya ce ya kama mutum ukun da laifin kisan kai da aikata fashi da makami.

Jagoran shigar da karar kuma tsohon kwamishinan shari’a na jihar Kwara, Barr. Salman Jawondo (SAN), wanda ya yi magana da ‘yan jarida bayan hukuncin ya yi karin haske da cewa bisa doka irin nau’in laifukan da wadanda ake zargi suka aikata hukuncin kisa ne ya dace da su bisa dogara da sashi na 221 na kundin laifuka.

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

“Wadanda ake zargi na hudu da na biyar an kamasu da laifin sace kudin mamaciyar a asusun ajiyarta. Bayan da suka kasheta, sun dauki na’urar cirar kudinta (ATM) da layukan wayarta. Sun canza lambobin sirri da hakan ya basu damar fitar da kudi har naira N149,000 daga asusun mamaciyar. An dauresu bisa laifin sata. An dauresu na tsawon shekara uku.”

“Sauran uku, wadanda ake tuhuma na shida, na bakwai da na takwas sun tsere

da wayo.”

Ya ce, idan aka duba shekarun wadanda suka aikata laifin da suke tsakanin shekara 19, 23 da saura abun takaici ne matuka.

Mutum takwas din da ake zargin su ne Abdulazeez Ismail, Ajala Moses Oluwatimileyin (da aka fi sani da Jacklord), Oyeyemi Timileyin Omogbolahan, Abdulkarim Shuaib (aka Easy), Kareem Oshioyemi Rasheed (Rashworld), Abdullateef Abdulrahman, Daud Bashir Adebayo (da aka fi sani da Bashman) da kuma Akande Taiye Oladoja.

LEADERSHIP ta labarto cewa rundunar ‘yansandan jihar Kwarai ta tabbatar da cewa an kashe Olajide ne a gidanta da ke Tanke a garin Illorin a ranar 2 ga watan June na 2021.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DalibaFyadeHunkunciJami'aKotu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Qatar 2022: Argentina Ta Je Matakin Wasan Karshe

Next Post

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

Related

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

3 days ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

3 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

3 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

4 weeks ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Next Post
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

LABARAI MASU NASABA

Son Zai Bar Tottenham Zuwa Amurka Bayan Shafe Shekaru 10 A Ingila

Son Zai Bar Tottenham Zuwa Amurka Bayan Shafe Shekaru 10 A Ingila

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.