ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 3 Hukuncin Kisa Kan Yi Wa Dalibar Jami’a Fyade

by Sadiq
4 years ago
Kotu

Kotu ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga mutum uku daga cikin mutum takwas da ake zargi da yin fyade da kashe dalibar Jami’ar Illorin mai shekara 24 a duniya, Olajide Blessing Omowumi, a ranar 2 ga watan Yuni, 2021.

Babbar kotun Jihar Kwara da ke zamanta a Ilorin ce ta yanke wannan hukuncin a ranar Talata.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 
  • Kanu Ya Yi Tur Da Kai Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Kudu Maso Gabas

Mutum uku da aka yanke wa hukuncin da wasu da ake zargi Gwamnatin Jihar Kwara ce ta gurfanar da su a gaban kotun cikin kara mai lamba KWS/33c/c/2021 dauke da tuhume-tuhume guda 11 da suka hada da fashi da makami, mallakar Malamai ba bisa ka’ida ba da kuma fyade hadi da sauran tuhume-tuhume.

ADVERTISEMENT

A hukuncin da mai shari’a Ibrahim Adebayo Yusuf, ya yanke ya ce ya kama mutum ukun da laifin kisan kai da aikata fashi da makami.

Jagoran shigar da karar kuma tsohon kwamishinan shari’a na jihar Kwara, Barr. Salman Jawondo (SAN), wanda ya yi magana da ‘yan jarida bayan hukuncin ya yi karin haske da cewa bisa doka irin nau’in laifukan da wadanda ake zargi suka aikata hukuncin kisa ne ya dace da su bisa dogara da sashi na 221 na kundin laifuka.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

“Wadanda ake zargi na hudu da na biyar an kamasu da laifin sace kudin mamaciyar a asusun ajiyarta. Bayan da suka kasheta, sun dauki na’urar cirar kudinta (ATM) da layukan wayarta. Sun canza lambobin sirri da hakan ya basu damar fitar da kudi har naira N149,000 daga asusun mamaciyar. An dauresu bisa laifin sata. An dauresu na tsawon shekara uku.”

“Sauran uku, wadanda ake tuhuma na shida, na bakwai da na takwas sun tsere

da wayo.”

Ya ce, idan aka duba shekarun wadanda suka aikata laifin da suke tsakanin shekara 19, 23 da saura abun takaici ne matuka.

Mutum takwas din da ake zargin su ne Abdulazeez Ismail, Ajala Moses Oluwatimileyin (da aka fi sani da Jacklord), Oyeyemi Timileyin Omogbolahan, Abdulkarim Shuaib (aka Easy), Kareem Oshioyemi Rasheed (Rashworld), Abdullateef Abdulrahman, Daud Bashir Adebayo (da aka fi sani da Bashman) da kuma Akande Taiye Oladoja.

LEADERSHIP ta labarto cewa rundunar ‘yansandan jihar Kwarai ta tabbatar da cewa an kashe Olajide ne a gidanta da ke Tanke a garin Illorin a ranar 2 ga watan June na 2021.

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

LABARAI MASU NASABA

Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026
Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.