ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 3 Hukuncin Kisa Kan Yi Wa Dalibar Jami’a Fyade

by Sadiq
4 years ago
Kotu

Kotu ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga mutum uku daga cikin mutum takwas da ake zargi da yin fyade da kashe dalibar Jami’ar Illorin mai shekara 24 a duniya, Olajide Blessing Omowumi, a ranar 2 ga watan Yuni, 2021.

Babbar kotun Jihar Kwara da ke zamanta a Ilorin ce ta yanke wannan hukuncin a ranar Talata.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 
  • Kanu Ya Yi Tur Da Kai Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Kudu Maso Gabas

Mutum uku da aka yanke wa hukuncin da wasu da ake zargi Gwamnatin Jihar Kwara ce ta gurfanar da su a gaban kotun cikin kara mai lamba KWS/33c/c/2021 dauke da tuhume-tuhume guda 11 da suka hada da fashi da makami, mallakar Malamai ba bisa ka’ida ba da kuma fyade hadi da sauran tuhume-tuhume.

ADVERTISEMENT

A hukuncin da mai shari’a Ibrahim Adebayo Yusuf, ya yanke ya ce ya kama mutum ukun da laifin kisan kai da aikata fashi da makami.

Jagoran shigar da karar kuma tsohon kwamishinan shari’a na jihar Kwara, Barr. Salman Jawondo (SAN), wanda ya yi magana da ‘yan jarida bayan hukuncin ya yi karin haske da cewa bisa doka irin nau’in laifukan da wadanda ake zargi suka aikata hukuncin kisa ne ya dace da su bisa dogara da sashi na 221 na kundin laifuka.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

“Wadanda ake zargi na hudu da na biyar an kamasu da laifin sace kudin mamaciyar a asusun ajiyarta. Bayan da suka kasheta, sun dauki na’urar cirar kudinta (ATM) da layukan wayarta. Sun canza lambobin sirri da hakan ya basu damar fitar da kudi har naira N149,000 daga asusun mamaciyar. An dauresu bisa laifin sata. An dauresu na tsawon shekara uku.”

“Sauran uku, wadanda ake tuhuma na shida, na bakwai da na takwas sun tsere

da wayo.”

Ya ce, idan aka duba shekarun wadanda suka aikata laifin da suke tsakanin shekara 19, 23 da saura abun takaici ne matuka.

Mutum takwas din da ake zargin su ne Abdulazeez Ismail, Ajala Moses Oluwatimileyin (da aka fi sani da Jacklord), Oyeyemi Timileyin Omogbolahan, Abdulkarim Shuaib (aka Easy), Kareem Oshioyemi Rasheed (Rashworld), Abdullateef Abdulrahman, Daud Bashir Adebayo (da aka fi sani da Bashman) da kuma Akande Taiye Oladoja.

LEADERSHIP ta labarto cewa rundunar ‘yansandan jihar Kwarai ta tabbatar da cewa an kashe Olajide ne a gidanta da ke Tanke a garin Illorin a ranar 2 ga watan June na 2021.

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.