ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 3 Hukuncin Kisa Kan Yi Wa Dalibar Jami’a Fyade

by Sadiq
3 years ago
Kotu

Kotu ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga mutum uku daga cikin mutum takwas da ake zargi da yin fyade da kashe dalibar Jami’ar Illorin mai shekara 24 a duniya, Olajide Blessing Omowumi, a ranar 2 ga watan Yuni, 2021.

Babbar kotun Jihar Kwara da ke zamanta a Ilorin ce ta yanke wannan hukuncin a ranar Talata.

  • Gwamnatin Ebonyi Ta Ba Da Umarnin Kashe Duk Wanda Aka Gani Da Bindiga 
  • Kanu Ya Yi Tur Da Kai Hare-Haren ‘Yan Bindiga A Kudu Maso Gabas

Mutum uku da aka yanke wa hukuncin da wasu da ake zargi Gwamnatin Jihar Kwara ce ta gurfanar da su a gaban kotun cikin kara mai lamba KWS/33c/c/2021 dauke da tuhume-tuhume guda 11 da suka hada da fashi da makami, mallakar Malamai ba bisa ka’ida ba da kuma fyade hadi da sauran tuhume-tuhume.

ADVERTISEMENT

A hukuncin da mai shari’a Ibrahim Adebayo Yusuf, ya yanke ya ce ya kama mutum ukun da laifin kisan kai da aikata fashi da makami.

Jagoran shigar da karar kuma tsohon kwamishinan shari’a na jihar Kwara, Barr. Salman Jawondo (SAN), wanda ya yi magana da ‘yan jarida bayan hukuncin ya yi karin haske da cewa bisa doka irin nau’in laifukan da wadanda ake zargi suka aikata hukuncin kisa ne ya dace da su bisa dogara da sashi na 221 na kundin laifuka.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

“Wadanda ake zargi na hudu da na biyar an kamasu da laifin sace kudin mamaciyar a asusun ajiyarta. Bayan da suka kasheta, sun dauki na’urar cirar kudinta (ATM) da layukan wayarta. Sun canza lambobin sirri da hakan ya basu damar fitar da kudi har naira N149,000 daga asusun mamaciyar. An dauresu bisa laifin sata. An dauresu na tsawon shekara uku.”

“Sauran uku, wadanda ake tuhuma na shida, na bakwai da na takwas sun tsere

da wayo.”

Ya ce, idan aka duba shekarun wadanda suka aikata laifin da suke tsakanin shekara 19, 23 da saura abun takaici ne matuka.

Mutum takwas din da ake zargin su ne Abdulazeez Ismail, Ajala Moses Oluwatimileyin (da aka fi sani da Jacklord), Oyeyemi Timileyin Omogbolahan, Abdulkarim Shuaib (aka Easy), Kareem Oshioyemi Rasheed (Rashworld), Abdullateef Abdulrahman, Daud Bashir Adebayo (da aka fi sani da Bashman) da kuma Akande Taiye Oladoja.

LEADERSHIP ta labarto cewa rundunar ‘yansandan jihar Kwarai ta tabbatar da cewa an kashe Olajide ne a gidanta da ke Tanke a garin Illorin a ranar 2 ga watan June na 2021.

MASU ALAKA

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja
Kotu Da Ɗansanda

An Kashe Wani Mamba Na NYSC A Harin Fashi Da Makami A Abuja

May 2, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum 7 Kan Satar Waya Da Fasa Gidaje A Jihar Yobe

April 25, 2026
An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Samun Gawar Wani Dan Nijeriya A Gidansa Da Ke Burtaniya

April 25, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

Kasar Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.