• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Koli Ta Tabbatar Lawal Dare A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Zamfara 

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Kotun Koli Ta Tabbatar Lawal Dare A Matsayin Dan Takarar Gwamnan PDP A Zamfara 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kotun kolin ta tabbatar da Dauda Lawal Dare a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Jihar Zamfara a zaben gwamnan jihar da za a yi ranar 11 ga watan Maris.

Alkalin kotun mai shari’a Adamu Jauro ne ya jagoranci, kwamitin alkalai biyar, ya yi watsi da karar da wani dan takarar gwamna, Dakta Ibrahim Gusau ya shigar kan zaben.

  • Sin Na Ci Gaba Da Dukufa Kan Bude Kofa Ga Ketare
  • Wani Soja Ya Hallaka Kwamandansa Ya Kuma Bindige Kansa Da Wasu Sojoji 2 A Sokoto

Ta tabbatar da abin da Mista Damian Dodo SAN, lauya ga Lawal Dare ya gabatar cewa an gabatar da wanda yake karewa bisa doka.

Jauro ya amince da hukuncin kotun daukaka kara da ta amince da zaben fidda gwani na biyu da ya samar da dan takarar.

A zaben fidda gwanin dai Lawal Dare ya samu kuri’u 442 inda ya samu nasara a kan Gusau da sauran ‘yan takara.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

Jauro ya ce wata babbar kotun tarayya da ke Gusau wadda ta soke zaben fidda gwani har sau biyu ba ta da hurumi a lokacin da ta yanke hukunci kan karar da Gusau ya shigar.

Zaben fidda gwani na gwamnan PDP na farko da aka gudanar a ranar 25 ga Mayu, 2022 an kalubalanci shi a wata babbar kotun tarayya da ke Gusau kuma ta soke shi.

A hukuncin da babbar kotun ta yanke ta bayar da umarnin sake gudanar da sabon zaben fidda gwani da aka gudanar a ranar 23 ga Satumba, 2022 amma kuma kotun ta soke shi saboda wasu kurakurai.

Bai gamsu da hukuncin babbar kotun ba, Dauda Lawal-Dare, Adamu Maina-Waziri, shugaban kwamitin zaben fidda gwani; sannan Kanar Bala Mande mai ritaya ya garzaya kotun daukaka kara domin neman tazarce.

Wadanda suka amsa karar sun hada da Dakta Ibrahim Shehu-Gusau, Alhaji Wadatau Madawaki, Hafiz Nuhuche da kuma Hukumar Zabe mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

A cikin hukuncin da aka yanke wanda mai shari’a Abubakar Talba a madadin wasu ya karanta, kotun daukaka kara ta ce wadanda suka shigar da kara sun yi nasarar tabbatar da dukkanin wasu dalilai guda bakwai na daukaka kara da lauyoyinsu suka yi masa, kuma kotun ta yanke hukuncin ga abin da ya dace.

Talba ya yi watsi da duk wani yunkuri na farko kan cancantar karar bisa tanadin shari’a da kuma sha’awar sauraren shari’a, yana mai cewa gazawar fasaha ba za ta iya maye gurbin tanadin shari’a ba.

Ya ce alkalin babbar kotun ya yi kuskure kan takardun rangwamen da INEC ta gabatar kuma kotun ba ta ayyana lokacin sake gudanar da zabe da kuma sanarwar shiga zabe ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KotuLawal DarePDPTakarar GwamnaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Ci Gaba Da Dukufa Kan Bude Kofa Ga Ketare

Next Post

Jam’iyyar NNPP Ta Bukaci Jami’an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

13 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

18 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

19 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

2 days ago
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Manyan Labarai

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

2 days ago
Next Post
Jam’iyyar NNPP Ta Bukaci Jami’an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

Jam'iyyar NNPP Ta Bukaci Jami'an Tsaro Su Tabbatar An Yi Sahihin Zabe A Kano

LABARAI MASU NASABA

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.