• English
  • Business News
Friday, September 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

by Sulaiman
3 weeks ago
in Ra'ayi Riga
0
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hausawa na cewa, “Mai nema na tare da samu”, a ranar 3 ga watan Satumban 2025, Sinawa yara da manya, samari da ’yan mata ta ko ina sun cika da farin cikin tunawa da wannan rana mai dimbin tarihi a rayuwar Sinawa, ita ce ranar da aka samu nasara a yaki da zalunci da danniya na Japanawa da suka mamaye yankunan Sinawa.

A bana, Sinawa na murnar cika shekaru 80 da samun wannan babbar nasara wacce juriya, jajircewa da hadin kai ya samar da ita bayan kai ruwa rana, wanda hankali ke dimauta da irin yadda aka cimma wannan nasara.

Saboda muhimnancin wannan rana, fiye da shugabannin kasashen waje 20 ne suka halarci bikin a dandalin Tian’anmen a birnin Beijing, wanda ya cika makil da jama’a, ga kuma an masa ado da kambun tarihin shekarar nasara “1945” da “2025”.

A wannan rana mai dimbin tarihi, rundunar soji ta jama’ar Sin ta gwangwaje duniya da fareti mai kayatarwa tare da baje kolin makamai masu linzami na zamani, jiragen yaki na sama da na ruwa, da sauran kayayyakin yaki na zamani don tunawa da wannan rana ta ’yan mazan jiya.

Yakin duniya na II shi ne mafi muni a tarihin yakin da dan adam ya taba yi. A duk duniya, mutane miliyan 70 zuwa 85 ne suka rasa rayukansu. An yi asarar kusan dala tiriliyan 4. A kasar Sin, shekaru 14 da aka shafe ana gwabzawa da jama’ar kasar Sin kan adawa da danniyar kasar Japan, ya yi sanadin jikkatawa da mutuwar sojoji da fararen hula fiye da miliyan 35, wannan sama da kashi daya cikin ukun wadanda suka mutu a yakin duniya II ke nan. Lallai sannu Sinawa, wato ko za a kare gaba daya, babu guduwa kuma ba mika wuya. A nan ne bahaushe ke cewa, “kowa ya ci zomo, ya ci gudu”.

Labarai Masu Nasaba

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

Yakin ya farkar da Sin da duniya baki daya, wanda ya zama tushen kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, daga bisani kuma ya dora kasar bisa tafarkin zamani. Ga duniya, mulkin mallaka ya fara wargajewa. Kasashe da dama sannu a hankali suka fahimci cewa, in sun jajirce, za su samu ‘yancin kai.

Tasirin yaki da zalunci da danniya da Jama’ar Sinawa suka yi, ya sa kasar ta kudiri aniyar yaki da zalunci da danniya a duniya ta rungumi manufar tabbatar da zaman lafiya, inda ta nuna wa duniya cewa, lokacin wariya da danniya, tsarin rayuwar dabbobi (na sama ya buge na kasa), ba zai dore ba amma samar da dawwamammen zaman lafiya da tsaro, na sama ya yi wa na kasa adalci, shi ne tsarin da ya dace kowa ya runguma.

Wannan fareti na nunawa duniya cewa, sojojin jama’ar kasar Sin an tanade su ne don tabbatar da zaman lafiya da aminci, inda yake a rubuce jikin alluna da tutoci, “Adalci zai yi nasara,” “samar da zaman lafiya zai yi nasara,” da kuma “mutane za su yi nasara”.

Daga cikin kasashe biyar na dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya (MDD), kasar Sin ta ba da gudummawar mafi yawan dakarun kiyaye zaman lafiya a fadin duniya.

A ’yan kwanakin nan, shugaban kasar Sin Xi Jinping a lokacin wani taron tattauna bukatun tsarin shugabancin duniya, ya yi nuni da cewa, kasar Sin za ta yi aiki kafada-da-kafada da kasashen duniya domin samar da “tsarin shugabanci na duniya mai adalci da daidaito”.

Wannan ya tabbatar da cewa, yakin da jama’ar Sinawa suka yi a kan yakin zalunci da danniya daga Japanawa bai tsaya nan kadai ba har ma da neman wa sauran kasashe masu tasowa ’yancin zaman lafiya da ci gaba mai dorewa.

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

Next Post

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

Related

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

1 day ago
Komai Nisan Dare Gari Zai Waye
Ra'ayi Riga

Komai Nisan Dare Gari Zai Waye

5 days ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

1 week ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

1 week ago
Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

2 weeks ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

3 weeks ago
Next Post
'Yan Bindiga

Sulhu Da 'Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

September 26, 2025
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

September 26, 2025
Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

September 26, 2025
’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

September 26, 2025
Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

September 26, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

September 26, 2025
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

September 26, 2025
An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

An Gano Cututtuka Uku Da Suka Ta Da Hankalin Hukumomin Lafiya A Nijeriya

September 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.